Aminiya:
2025-10-13@13:32:22 GMT

Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano

Published: 10th, October 2025 GMT

Hukumar Tsaro ta Sibil Difens a Jihar Kano, ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a Ƙaramar Hukumar Doguwa.

Hukumar ta miƙa su ga Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), domin ci gaba da bincike da gurfanar da su a kotu.

’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno

Kwamandan hukumar na Jihar Kano, Bala Bawa Bodinga ne, ya bayyana hakan yayin da yake magana da ’yan jarida a hedikwatar hukumar a ranar Juma’a.

Ya ce an kama mutanen ne da sanyin safiyar ranar Talata, 7 ga watan Oktoba, 2025, bayan samun sahihin bayaai.

Jami’an hukumar daga sashen Doguwa sun tare su a ƙofar Riruwai da ke Doguwa yayin da suke ɗauke da manyan jakunkuna uku cike da tabar wiwi.

Babban wanda ake zargi shi ne Yusuf Alasan, mai shekara 25, tare da abokan aikinsa biyu; Muktar Musa da Musa Sani.

Kwamandan, ya ce hukumar ta kammala binciken farko kuma ta miƙa su tare da kayan da aka kama zuwa ofishin NDLEA na Jihar Kano don yin ƙarin bincike.

Bodinga, ya ƙara da cewa NSCDC za ta ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin kawar da laifuka da tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Doguwa Ƙwaya Safara zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe

A yayin da ake yawan samun ɓarnar dorinar ruwa a garuruwan Daɗin Kowa da Kupto da Malleri da Wade a yankunan Ƙananan hukumomin Kwami da Yamaltu Deba a Jihar Gombe ta kai ga samun asarar amfanin gona da rayuka.

Hakan ne ya sa Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Yamaltu/ Deba a Jihar Gombe Inuwa Garba ya gabatar da ƙudiri a gaban zauren Majalisar Wakilai ta tarayya domin neman ɗaukar matakin gaggawa kan ɓarnar dorinar ruwa.

’Yan sanda sun ceto mutum 3 da aka sace a Kano da Kaduna Kwastam ta kama buhunan lalatacciyar fulawa 10,000 ana ƙoƙarin shigo da ita Najeriya

Inda ya ce dorinar na yi wa manoma ɓarna sosai da ke janyo asarar rayuka, dukiyoyi da lalacewar amfanin gona a yankunan da abin ya shafa.

Inuwa Garba ya bayyana hakan ne, a shafinsa na Facebook cewa, dorinar ruwan ta zama babbar matsala ga manoma da al’ummomin waɗannan yankuna inda ake samun girgizar tattalin arziki sakamakon lalacewar gonaki, lalata hanyoyi da kuma rasa muhallin zama.

Ya ce, wannan ƙudiri na da nufin kawo mafita ta dindindin domin kare rayukan mutane, kiyaye dukiyoyin su da kuma tabbatar da ci gaban noman rani da damina, wanda shi ne tushen rayuwar yawancin mazauna yankin.

Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Gombe, tare da hukumomin kula da ruwa da su kai ɗauki cikin hanzari ta hanyar bayar da tallafi, gyaran madatsun ruwa da kuma samar da hanyoyin rage haɗarin dorinar a nan gaba.

A ƙarshe, ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalai da ‘yan uwa na waɗanda suka rasa rayukansu a ibtila’in dorinar ruwa yana roƙon Allah Ya jikan mamatan da rahama, tare da ba iyalansu haƙuri, juriya na rashin da suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
  • Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe
  • Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano