Aminiya:
2025-11-27@21:12:43 GMT

’Yan sanda sun ceto mutum 3 da aka sace a Kano da Kaduna

Published: 10th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta samu nasarar ceto wasu mutum uku da aka sace, bayan wani samame da ta kai a jihohin Kano da Kaduna.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin da rundunar ke yi domin yaƙi da laifuka da tabbatar da tsaron jama’a.

’Yan sanda sun manta hularsu a motar dalibi bayan karɓar ‘cin hancin’ N99,000 NAJERIYA A YAU: Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Zabe Ta Kasa

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya bayyana cewa an gudanar da samamen ne tsakanin ranar 7 zuwa 9 ga watan Oktoba, 2025, bisa umarnin Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori.

A cewar Kiyawa, samamen farko ya gudana ne a ranar 7 ga watan Oktoba.

Ya ce runduna ta musamman ta yaƙi da garkuwa da mutane tare da haɗin gwiwar tawagar sintiri ta sashen ’yan sanda na Bebeji suka kai samame, bayan samun bayanan sirri.

An ceto mutanen ne, bayan wani matashi mai shekaru 21, mai suna AbdulHamid Bello, wanda aka sace, ya yi nasarar tserewa daga hannun masu garkuwa da shi, ya sanar da ’yan sanda inda aka ajiye shi.

Wannan ya taimaka wajen gani maɓoyar masu garkuwar da ke ƙauyen Saya-Saya, a Ƙaramar Hukumar Ikara ta jihar Kaduna, inda suka samu nasarar ceto wani mutum mai suna Musa Idris, mai shekaru 65.

Masu garkuwar sun tsere bayan ganin ’yan sanda, inda suka bar babur da igiya.

Daga baya, an mayar da waɗanda aka ceto zuwa ga iyalansu tare da kai su asibiti don kula da su.

A wani lamari daban da ya faru a ranar 9 ga watan Oktoba, ’yan sanda sun kuma ceto wani matashi mai shekaru 19 mai suna Ashiru Murtala, wanda aka sace a ranar 5 ga watan Oktoba a ƙauyen Beli da ke Ƙaramar Hukumar Rogo ta Jihar Kano.

Masu garkuwar sun bar shi a gonar rake da ke Hunkuyi,a Jihar Kaduna, inda ’yan sanda suka same shi cikin ƙoshin lafiya.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya umurci a kula da lafiyar waɗanda aka ceto, tare da tabbatar da cewa rundunar tana ci gaba da neman waɗanda suka tsere.

“Babu wajen ɓoyewa ga masu laifi a Jihar Kano,” in ji CP Bakori, inda ya yaba wa jarumtaka da ƙwazon jami’an da suka kai samamen.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane ga watan Oktoba

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.

Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.

Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja