’Yan sanda sun ceto mutum 3 da aka sace a Kano da Kaduna
Published: 10th, October 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta samu nasarar ceto wasu mutum uku da aka sace, bayan wani samame da ta kai a jihohin Kano da Kaduna.
Wannan na daga cikin ƙoƙarin da rundunar ke yi domin yaƙi da laifuka da tabbatar da tsaron jama’a.
’Yan sanda sun manta hularsu a motar dalibi bayan karɓar ‘cin hancin’ N99,000 NAJERIYA A YAU: Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Zabe Ta KasaA cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya bayyana cewa an gudanar da samamen ne tsakanin ranar 7 zuwa 9 ga watan Oktoba, 2025, bisa umarnin Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori.
A cewar Kiyawa, samamen farko ya gudana ne a ranar 7 ga watan Oktoba.
Ya ce runduna ta musamman ta yaƙi da garkuwa da mutane tare da haɗin gwiwar tawagar sintiri ta sashen ’yan sanda na Bebeji suka kai samame, bayan samun bayanan sirri.
An ceto mutanen ne, bayan wani matashi mai shekaru 21, mai suna AbdulHamid Bello, wanda aka sace, ya yi nasarar tserewa daga hannun masu garkuwa da shi, ya sanar da ’yan sanda inda aka ajiye shi.
Wannan ya taimaka wajen gani maɓoyar masu garkuwar da ke ƙauyen Saya-Saya, a Ƙaramar Hukumar Ikara ta jihar Kaduna, inda suka samu nasarar ceto wani mutum mai suna Musa Idris, mai shekaru 65.
Masu garkuwar sun tsere bayan ganin ’yan sanda, inda suka bar babur da igiya.
Daga baya, an mayar da waɗanda aka ceto zuwa ga iyalansu tare da kai su asibiti don kula da su.
A wani lamari daban da ya faru a ranar 9 ga watan Oktoba, ’yan sanda sun kuma ceto wani matashi mai shekaru 19 mai suna Ashiru Murtala, wanda aka sace a ranar 5 ga watan Oktoba a ƙauyen Beli da ke Ƙaramar Hukumar Rogo ta Jihar Kano.
Masu garkuwar sun bar shi a gonar rake da ke Hunkuyi,a Jihar Kaduna, inda ’yan sanda suka same shi cikin ƙoshin lafiya.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya umurci a kula da lafiyar waɗanda aka ceto, tare da tabbatar da cewa rundunar tana ci gaba da neman waɗanda suka tsere.
“Babu wajen ɓoyewa ga masu laifi a Jihar Kano,” in ji CP Bakori, inda ya yaba wa jarumtaka da ƙwazon jami’an da suka kai samamen.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane ga watan Oktoba
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Iran tana goyon bayan duk wani Shirin zaman lafiya da ya hada da dakatar da kisan kiyashi a Gaza
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta tabbatar da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana goyon bayan duk wani mataki ko wani yunkuri da ya hada da kawo karshen yakin kisan kiyashi a Gaza, janyewar sojojin mamayar Isra’ila, shigar da kayan agajin jin kai, sakin fursunonin Falastinawa, da kuma tabbatar da dukkanin hakkokin Falasdinawa.
Haka kuma ta kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mai goyon bayan halastacciyar gwagwarmayar al’ummar Falastinu samun tabbatar da ‘yancin kai, ta yi amfani da dukkanin karfinta na diflomasiyya a cikin shekaru biyun da suka gabata, musamman a matakin yanki, kungiyar hadin kan kasashen musulmi, da Majalisar Dinkin Duniya, wajen matsin lamba ga yahudawan sahayoniyya da magoya bayansu da su dakatar da kisan kiyashi da kuma janyewar ‘yan mamaya daga Gaza.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta yi juyayin tunawa da manyan shahidan gwagwarmaya, inda ta jaddada nauyin da ke wuyan kasashen duniya na hana duk wani cin zarafi daga ‘yan mamaya, tare da yin kira ga dukkan bangarorin da su yi taka tsantsan da yaudara da karya alkawari da sahayoniyya suke yi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci