Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN
Published: 10th, October 2025 GMT
“Akwai da yawa malamai marasa cancanta a cikin aikin. Muna da wadanda ke koyarwa a ajujuwa amma ba su da takardun shaidar koyarwa, musamman a makarantu masu zaman kansu,” in ji ta.
Ta bayyana cewa, yayin da wasu mutane ke da sha’awar koyarwa da gaske, rashin horo na hukuma ya hana su shiga aikin koyarwa.
Dr. Soyombo ta bayyana cewa TRCN a halin yanzu na da malamai masu rijista kusan miliyan 1.4, tare da shirin kara wannan adadi zuwa miliyan 20 cikin shekaru biyu masu zuwa ta hanyar dijital da saurin rajista.
“Mun zamanantar da tsarinmu domin mutane da yawa su sami damar yin rijista,” in ji ta. “Kowane malami yana da bai wa ta musamman wadda ta bambanta da ta wani. Amma abin da muke kokarin yi domin inganta ilimi shi ne kowa ya zo tare da tsarinsa na darussa.”
“Za ku iya zama malamai uku da ke koyarwa ga rukuni guda na dalibai, kuma idan kuka zo tsara darusa tare tabbas za ku samar da wani abu mai dimbin fa’ida fiye da lokacin da kake aiki kai kadai.”
“Babu shakka akwai karancin malamai, don haka abin da muke yi tare da wannan gwamnati shi ne gaggauta shirin Diploma na Kwarewa a Fannin Ilimi (PDE). Ga wadanda ba su da shi, yanzu lokaci ne da za su iya samun dama. Muna gaggauta kwas din zuwa watanni shida ga malamai masu kwarewa, domin da zaran sun kammala, za su sami kwarewa. Wannan zai sa mu samu isassun ma’aikata a fannin koyarwa.”
“Abin da TRCN ke yi kuma shi ne duba yadda za mu inganta malamai. Haka kuma, muna tallafa musu da kayan aiki a cikin ajujuwa, domin wasu malamai suna da kwarewa sosai kuma suna neman yadda za su tsara darussa don tallafawa sauran malamai, kuma hakan zai karfafa wasu su shigo,” in ji ta.
A halin da ake ciki, Uwargidan Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, a cikin sakonta na Ranar Malamai ta Duniya, ta yaba wa malamai kan gudummawar da ba za a iya misaltawa ba wajen gina kasa, sannan ta yi kira ga kokari na musamman don magance karancin malamai a duniya.
Tinubu ta bayyana malamai a matsayin “jarumai, masu tsara tunani, da jagorantar karni,” inda ya jaddada cewa inganta walwalarsu da ci gaban kwarewarsu na aiki shi ne mabudin karfafa tsarin ilimi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
Gwamnonin jihohin Arewa 19 za su gudanar da muhimmin taro a ranar Asabar, 29 ga Nuwamba, domin tattauna matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
Mai bai wa Gwamnan Nasarawa shawara na musamman kan harkokin jama’a, Peter Ahemba, ne ya sanar cewa, taron gwamnonin Arewa da aka shirya a Kaduna zai samu halartar manyan sarakunan gargajiya.
“Manufar taron ita ce samar da matsaya ɗaya wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke damun yankin, tare da tsara hanyar magance su,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, za a yanke muhimman shawarwari a taron domin tabbatar da tsaron yankin.
’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a KatsinaAhemba ya bayyana cewa, sakamakon ƙalubalen tsaro da wasu jihohin Arewa ke fuskanta, gwamnatin Nasarawa ta ɗauki matakan gaggawa ta hanyar shirya taron tsaro na musamman, inda za a yanke shawarar da za ta kare jihar daga duk wata barazanar tsaro.
“Ya zama wajibi ga ’yan ƙasa su taka rawa wajen magance barazanar tsaro a ƙasarmu da jihohinmu. Don haka, dole ne jama’a su riƙa ba wa hukumomin tsaro bayanai kan mutanen da ke da halin aikata laifi,” in ji shi.