Tawagar da ke karkashin jagorancin, Barry Andrews ta kuma ziyarci hedkwatar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), inda shugabanta, Mahmood Yakubu, ya yi gargadin cewa jinkirin da ‘yan majalisa ke yi wajen gyaran dokar zabe ta 2022 na iya kawo cikas ga shirye-shiryen gudanar da zabe a 2027.

 

Wakilan, wadanda suke Nijeriya tun kusan makonni uku domin nazarin matakin aiwatar da shawarwarin da ke cikin rahotonsu na bayan zaben 2023, sun kuma yi tattauna da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.

 

Abbas, a cikin wata sanarwar da sakataren yada labaransa, Leke Bayeiwu, ya shaida wa tawagar EU cewa rahotanninta kan zabukan shekarar 2023 ana la’akari da su a cikin sauye-sauyen gyara dokar zabe da na dimokuradiyya da Majalisar dokoki ke gudanarwa.

 

Abbas ya ce, “Ina so in bayyana cewa shugabancin kasar nan karkashin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yana kokarin tabbatar da cewa mun inganta tsarin zabenmu, musamman game da abubuwan da masu saka ido na kasashen waje suka lura da su a lokacin zaben 2023.

 

“Mu a majalisar kasa ma mun kasance cikin aiki tukuru wajen tattara mafi yawan batutuwa da suka taso daga zaben 2023, domin mu ga yadda za mu iya magance su ta hanyar bin dokoki, domin zabenmu na gaba ya kasance mai inganci da amsuwa a idon duniya.”

 

Ya shaida wa tawagar cewa taron shugabannin majalisar dattawa da na majalisar wakilai da aka yi kwanan nan ya yanke shawarar warware batutuwan gyaran tsarin zabe cikin hanzari.

 

Ya bayyana cewa ra’ayin da yawa daga ‘yan majalisar kasa shi ne, gudanar da zabe a rana guda ba wai kawai zai kara inganci da gaskiya a gudanar da zaben kadai ba, har ma zai rage yawan kashe kudade na kusan kashi 40 cikin dari.

 

Ya ce, “Kamar gudanar da zabe a rana daya, wanda zai bayar da damar gudanar da zaben shugaban kasa da mambobin majalisar tarayya da gwamnonin jihohi da kuma ‘yan majalisar dokoki na jihohi duka a rana guda.

 

“A tunaninmu, zai taimaka wajen rage kashe kudaden gudanar da zabenmu har kashi 40 cikin ddari idan muka iya gudanar da zabukan cikin rana guda. Hakan zai kuma inganta gaskiya da karfafa aiki yadda ya kamata, musamman wajen fitowar masu kada kuri’a.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tambarin Dimokuradiyya 2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe October 10, 2025 Tambarin Dimokuradiyya ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu October 3, 2025 Tambarin Dimokuradiyya Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar October 3, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gudanar da zabe

এছাড়াও পড়ুন:

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

A bisa wannan dalilin, ya kuma zama waji, manyan hafsohin tsaron su mayar da hankali, wajen ingnata jin dadi da walwalar dakarun sojin, musamman duba da cewa, manyan hafsoshin tsaron, su ba baki ne, kan wadannan kalubalen ba, domin kuwa kafin nada su, a baya an nada su kan makamai da ban da ban.

Kwarewar da kuma ilimin da suke da shi, a aikin soji, abu ne da zai taimaka masu wajen sauke nauyin da aka dora masu.

Abu na biyu shi ne, akwai bukatar a tsakaninsu, su hada karfi da karfe, domin su samu nasarar tunkarar aikin da ke a gabasu na tabbatar da tsaro a kasar, ba wai su rinka yi aiki, a daidaikunsu ba.

Kazalika, dole na rundunar sojin sama ta taimaka wa rundunar soji na kasa da kuma na ruwa, a yayin duka wani farmaki, tare da kuma yin musayar bayanai, a tsakansu.

Na ukun shi ne, dole ne su mayar da hankali kan samar dabaru, yayin gudanar da ayyukansu, musamman duba da irin sarkakiyar da ke tattare da yanayin kalubalen rashin tsaron kasar, misali duba da irin salon ayyukan ‘yan bindiga daji da masu garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan ta’adda, na kai hare –hare, wanda a yanayi irin wannan akwai matukar a dauki dabarun magance wannan barazanar ta su.

Yakar ta ‘yan bindiga daji da masu garkuwa da mutane da kuma masu aikata manyan laifuka, ya zarce ace manyan hafsoshin tsaro ne kadai za su yi hakan, domin kuwa, akwai kuma bukatar su tabbatar da sun samu goyon bayan alummar gari, musamman ta hanyar samun bayanan sirri.

Bugu da kari, na hudun shi ne, su tabbatar da dakarunsu na kai farmaki ta kasa duba da cewa, akasarin kalubalen rashin rashin tsaron ya ta’allaka ne na kasa, musamman duba da cewa maboyar ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga daji, a kan doron kasa suke.

Dole ne manyan hafsoshin tsaron su sanya a zuciyarsu na cewa, su masu yin biyayya ne, ga kundun tsarin mulkin kasar kuma dole ne su kare su tabbatar da sun kare dorewar mulkin dimokaradiyyar kasar.

Kazalika, ya zama wajbi, a tantace a tsakanin ayyukan soji na kuma na siyasa.

A saboda haka ne, ba ma goyon bayan soji yin kutse a cikin batun abinda ya shafi fanin siyasa, musamman duba da cewa, kasashen da soji suka shiga cikin lamarin siyasa, sun kasance, ba su ji dadi ba, kuma bai kamata Nijeriya ta kasance a cikin jerin irin wadannan kasashen ba.

Wannan Jaridar na shawartar ‘yan siyasar kasar nan, kar su kutsa kansu kan batun da ya shafi lamuran ayyukan sojin kasar, musamman gwamnonin jihohin kasar, musamman duba da cewa, mun lura da irin wannan shishigin na wasu ‘yan siyasar kasar inda suke bayyana gazawar da sojin kasar ke yi, na tabbatar da tsaro a kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4 November 13, 2025 Manyan Labarai Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2 November 13, 2025 Manyan Labarai Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su November 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
  • Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
  • Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu
  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Iraki: Hukumar Zabe Ta Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar
  • Majalisa ta amince da buƙatar Tinubu na karɓo rancen N1.15bn
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu