2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe
Published: 10th, October 2025 GMT
“Muna kira ga majalisar kasa da ta yi la’akari da shirin gyaran tsarin kudurorin zabe cikin gaggawa. Amincewa da dokar cikin lokaci yana da muhimmanci ga shirinmu na gudanar da zabe a 2027.
“Rashin tabbas game da tsarin doka na zabe na iya kawo matsaloli masu yawa ga ayyukan hukumar INEC yayin da lokacin zabe ke karatowa,” in ji shi.
Shugaban INEC ya bayyana cewa hukumarsa ta aiwatar da shawarwarin da aka mika mata kai tsaye a rahoton EU na zaben 2023.
“An dauki mataki kan wasu bangarori na shawarwarin da ake bukatar hukumar ta aiwatar da su. Haka kuma, ana daukar mataki kan shawarwarin da suka shafi fannoni da dama wadanda ake bukatar hadin gwiwa tsakanin INEC da sauran hukumomi da masu ruwa da tsaki yayin da ake jiran kammala bitar sake fasalin shari’a da majalisar kasa ke yi,” in ji shi.
A nasa kalamun, Mista Barry Andrews ya yaba da muhimmancin Nijeriya a dimokuradiyyar duniya, yana bayyana aikin EU na 2023 a matsayin daya daga cikin manyan aikace-aikace ga dukkan kasashen duniya.
“Aikinmu shi ne taimakawa wajen samun ci gaban na aiwatar da shawarwarin daga zabukan shekarar 2023. Mun lura da manyan ci gaba a wasu fannoni da dama, ko da yake wasu kalubale suna nan yadda suke, musamman wadanda suka shafi shari’a da gudanarwa da tsarin gyara fasalin kundin tsarin mulki,” in ji shi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: shawarwarin da
এছাড়াও পড়ুন:
MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC
Kungiyar Kare Muradun Musulmai (MURIC) ta bukaci a gaggauta tsige Farfesa Joash Amupitan daga shugabancin Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), saboda matsayinsa kan batun rashin tsaro a Najeriya.
Aminiya ta rawaito cewa, a cikin wani rubutu a baya, Amupitan wanda a lokacin malami ne a Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya ce “abu ne sananne cewa ana aikata laifuka a ƙarƙashin dokokin kasa da kasa a Najeriya, musamman laifukan da suka shafi cin zarafin bil’adama, laifukan yaki da kuma kisan kare dangi.”
Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin KanoYa kara da cewa: “Kalma guda da hukumomin Najeriya da masu bincike na kasa da kasa da masu bayar da rahoto ba su ambata ba (ko kuma suka ki ambata) dangane da dogon rikicin da ake fama da shi a Najeriya ita ce ‘kisan kare dangi.’ Shin wannan mantuwa ce ta gangan ko kuskure ne?
“Zargin shiga tsakanin gwamnati da kungiyoyin da ba na gwamnati ba wajen aikata laifukan kasa da kasa a Najeriya ya kara dagula lamarin da tuni ya yi tsauri.
“Kungiyar Boko Haram tana da burin sauya Najeriya zuwa tsarin Musulunci. ’Yan bindigar kabilar Fulani, a nasu bangaren, sun shiga irin wannan rikicin na adawa da Kiristoci kamar yadda Boko Haram ke yi,” kamar yadda ya rubuta a lokacin.
Haka kuma ya kira Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, hukumomin majalisar da manyan kasashen duniya da su shawarci kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar kisan kare dangi su kai Najeriya kotun kasa da kasa (ICJ) saboda gazawar ta wajen hana da hukunta kisan kare dangi kamar yadda aka tanada a cikin saɗarori na 8 da 9 na yarjejeniyar; sannan su yi la’akari da shigar dakarun Majalisar Dinkin Duniya, Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ko na ECOWAS a matsayin mataki na karshe, bisa ga saɗara ta 42 a Kundin Majalisar Dinkin Duniya.
To sai dai a cikin wata sanarwa da shugabanta, Farfesa Ishaq Akintola ya fitar, MURIC ta gargadi cewa duk wanda ya shafi irin wannan rubutu mai cike da cece-kuce ba za a iya amincewa da shi wajen jagorantar harkokin zabe ba a Najeriya.
“Mutumin da ya rubuta wasikar kiyayya ga Shugaba Donald Trump kan Musulmai a Arewacin Najeriya ba za a iya tsammanin adalci daga gare shi wajen gudanar da zabe a Najeriya ba,” in ji shi.
MURIC ta ce rawar da ake zargin shugaban INEC ya taka a cikin rahoton ta lalata amincewar da jama’a suka yi masa a baya kuma tana haifar da “barazana ga Musulmai ’yan takara a Arewa ta Tsakiya da sauran sassan kasar.”
“Tun daga lokacin da wannan bayani ya fito, Amupitan ya zama wanda Musulmai ba sa son ganin ya taka rawa a harkokin zabe. Muna bayyana cikakkiyar rashin amincewa da shi a matsayin shugaban INEC,” in ji kungiyar.
Kungiyar ta kuma bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya tsige shugaban INEC daga muƙaminsa tare da nada wanda zai samu karɓuwa a fadin kasa.
“Muna ba da shawarar cewa a zabi wani wanda ya cancanta, da zai samu karbuwa a fadin kasa, wanda zai fi dacewa ya kasance mai addini daya da Amupitan amma daga wani yanki daban na siyasa,” in ji Akintola.