Wata kafar labarai daban, Peoples Gazette, tun da farko a shekarar 2024, ta ruwaito labaran da ke zarginsa da yin jabun takardar shaidar NYSC.

 

Sai dai Nnaji ya karyata labarin da Premium Times ta wallafa, yana mai cewa zargin aiki ne na abokan hamayyar siyasa a Jiharsa ta Enugu.

 

Tsohon ministan, wanda aka nada a watan Agusta 2023, ya mika takardar murabus dinsa a ranar Litinin ga Shugaban Kasa, inda ya nuna godiyarsa kan damar da aka ba shi ta yi wa kasa hidima.

 

A cikin wasikar tasa, tsohon ministan ya bayyana cewa ya zama abin kai hare-hare na “tsananin batanci” daga abokan hamayyar siyasa da ke neman bata masa suna.

 

“Ina gode wa Shugaban Kasa bisa amincewa da ni da kuma damar da ya ba ni na bayar da gudunmawa ga ci gaban kasa,” in ji Nnaji, yana mai kara da cewa yana janyewa ne don kare mutuncin gwamnatin.

 

Shugaba Tinubu, yayin da ya amince da murabus dinsa, ya yaba wa Nnaji bisa hidimar da ya bayar ga kasa tare da yi masa fatan alheri a harkokinsa na gaba.

 

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa matsin lamba na karuwa kan ministan bayan da jami’ar Unibersity of Nigeria, Nsukka (UNN) ta nesanta kanta daga takardar shaidar da ake zargin Nnaji ya gabatar.

 

A cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 2 ga Oktoba, 2025, wadda Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfa Simon Ortuanya, ya sanya wa hannu, jami’ar ta bayyana cewa bayanan da ke hannunta sun nuna cewa Nnaji, mai lambar shigar makaranta 1981/30725, an karbe shi a shekarar 1981 domin karatun Microbiology/Biochemistry, amma bai kammala karatunsa ba.

“Saboda haka, Jami’ar Nijeriya, Nsukka ba ta taba bayar da takardar shaidar da ake ikirari a watan Yuli 1985 ga Mista Geoffrey Uchechukwu Nnaji ba, kuma ba za ta iya bayar da ita ba,” in ji jami’ar.

Jami’ar ta ce wannan matsayi nata ya yi daidai da abin da ta bayyana a cikin wata wasika da ta aike wa Hukumar Karbar Korafe-korafe ta Jama’a a ranar 13 ga Mayu, 2025, a matsayin amsa ga irin wannan tambaya da aka yi a baya.

Sai dai a cikin takardarsa da ya gabatar gaban kotu, Nnaji ya amince cewa har yanzu bai karbi takardar shaidar digirinsa daga jami’ar ba, inda ya danganta jinkirin da abin ya samu ga abin da ya kira “rashin hadin kai” daga jami’an UNN.

Fadar Shugaban Kasa ta bayyana cewa ba za ta dauki mataki kan lamarin ba saboda shari’ar tana gaban kotu.

Sai dai, Cif Uche Nnaji ya riga ya karyata zargin jabun takardar shaidar karatu da aka yi masa, inda ya nemi hukumar jami’ar da ta saki takardar shaidar karatunsa.

A yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin, ministan ya bayyana cewa zargin jabun takarda na da tushe na siyasa, kuma an tsara shi ne da nufin bata masa suna kafin zaben gwamna na 2027 a jiharsa.

A halin yanzu, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsara ranar 10 ga Nuwamba domin sauraron karar da Minista Nnaji ya shigar kan Jami’ar UNN.

Ministan ya shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1909/2025 ne sakamakon zargin jabun takardar shaida da aka yi masa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC October 10, 2025 Labarai Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe October 10, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: takardar shaidar bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro da ta addabi dukkan sassa a Nijeriya.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin wannan Larabar mai ɗauke da sa hannunsa, Tinubu ya bayyana cewa dole ne a ɗauki matakan gaggawa da suka dace domin fuskantar barazanar tsaro da ke ƙaruwa ƙasar nan.

Shugaban ya bayar da umarnin ɗaukar ƙarin jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an ’yan sanda 20,000, lamarin da zai ƙara adadin jami’an da za a ɗauka zuwa 50,000, bayan umarnin da ya bayar a ranar Lahadi na ɗaukar jami’an tsaro 30,000.

Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu

Haka kuma, Tinubu ya bai wa rundunar sojin ƙasa da sauran hukumomin tsaro umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai.

Sanarwar ta ce za a yi amfani da sansanonin masu yi wa ƙasa hidima NYSC a matsayin wuraren horas da sabbin ’yan sandan.

Kazalika, shugaban ya bai wa hukumar ’yan sandan farin kaya ta DSS umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai a rundunar kare dazuka wato Dakarun Gandun Daji ta Forest Guard.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci DSS ta aika dakarun Forest Guard “domin zaƙulo ’yan ta’adda da ’yan fashi daga dazuka.”

“Babu wani sauran gidan ɓuya ga miyagu,” in ji shi kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ta bayyana.

Sanarwar ta ƙara da cewar, za a sake horar da jami’an ’yan sanda da aka janye daga gadin fitattun mutane kafin mayar da su aikin ɗan sandan gada-gadan.

Shugaban ya yi amfani da damar wajen jinjinawa hukumomin tsaro wajen kuɓutar da mutane 34 da aka sace a Mujami’ar Kwara da ɗalibai 24 da aka sace a makarantar jihar Kebbi, yayin da ya ce suna ɗaukar matakan da suka dace wajen kuɓutar da ɗaliban makarantar mabiya ɗarikar Katolika da ke Jihar Neja.

Tinubu ya jinjinawa rundunar sojin ƙasar a kan gudumawar da jami’anta ke bayarwa da kuma gabatar da ta’aziyar rasuwar Janar Musa Uba da ƴanta’adda suka yiwa kisan gilla, yayin da ya buƙace su da su ƙara ƙaimi wajen tabbatar da tsaro a yankunan da ake fama da tashin hankali.

Shugaban ya buƙaci majalisar ƙasa da ta sake fasalin dokokin tsaro domin bai wa jihohi damar samar da ’yan sanda na kashin kan su, yayin da ya ce gwamnatin tarayya za ta taimaka musu.

Tinubu ya kuma buƙaci Masallatai da Majami’u da su dinga neman taimakon jami’an tsaro a duk lokacin da za su gudanar da taron ibadun su, musamman a yankunan da ake fama da matsalar tsaro.

Shugaban ya kuma jajanta wa gwamnatoci da kuma mutanen jihohin Kebbi da Borno da Zamfara da Neja da Yobe da kuma Kwara saboda kisan gillar da ƴan ta’adda suka yiwa mutanen su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina