Wata kafar labarai daban, Peoples Gazette, tun da farko a shekarar 2024, ta ruwaito labaran da ke zarginsa da yin jabun takardar shaidar NYSC.

 

Sai dai Nnaji ya karyata labarin da Premium Times ta wallafa, yana mai cewa zargin aiki ne na abokan hamayyar siyasa a Jiharsa ta Enugu.

 

Tsohon ministan, wanda aka nada a watan Agusta 2023, ya mika takardar murabus dinsa a ranar Litinin ga Shugaban Kasa, inda ya nuna godiyarsa kan damar da aka ba shi ta yi wa kasa hidima.

 

A cikin wasikar tasa, tsohon ministan ya bayyana cewa ya zama abin kai hare-hare na “tsananin batanci” daga abokan hamayyar siyasa da ke neman bata masa suna.

 

“Ina gode wa Shugaban Kasa bisa amincewa da ni da kuma damar da ya ba ni na bayar da gudunmawa ga ci gaban kasa,” in ji Nnaji, yana mai kara da cewa yana janyewa ne don kare mutuncin gwamnatin.

 

Shugaba Tinubu, yayin da ya amince da murabus dinsa, ya yaba wa Nnaji bisa hidimar da ya bayar ga kasa tare da yi masa fatan alheri a harkokinsa na gaba.

 

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa matsin lamba na karuwa kan ministan bayan da jami’ar Unibersity of Nigeria, Nsukka (UNN) ta nesanta kanta daga takardar shaidar da ake zargin Nnaji ya gabatar.

 

A cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 2 ga Oktoba, 2025, wadda Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfa Simon Ortuanya, ya sanya wa hannu, jami’ar ta bayyana cewa bayanan da ke hannunta sun nuna cewa Nnaji, mai lambar shigar makaranta 1981/30725, an karbe shi a shekarar 1981 domin karatun Microbiology/Biochemistry, amma bai kammala karatunsa ba.

“Saboda haka, Jami’ar Nijeriya, Nsukka ba ta taba bayar da takardar shaidar da ake ikirari a watan Yuli 1985 ga Mista Geoffrey Uchechukwu Nnaji ba, kuma ba za ta iya bayar da ita ba,” in ji jami’ar.

Jami’ar ta ce wannan matsayi nata ya yi daidai da abin da ta bayyana a cikin wata wasika da ta aike wa Hukumar Karbar Korafe-korafe ta Jama’a a ranar 13 ga Mayu, 2025, a matsayin amsa ga irin wannan tambaya da aka yi a baya.

Sai dai a cikin takardarsa da ya gabatar gaban kotu, Nnaji ya amince cewa har yanzu bai karbi takardar shaidar digirinsa daga jami’ar ba, inda ya danganta jinkirin da abin ya samu ga abin da ya kira “rashin hadin kai” daga jami’an UNN.

Fadar Shugaban Kasa ta bayyana cewa ba za ta dauki mataki kan lamarin ba saboda shari’ar tana gaban kotu.

Sai dai, Cif Uche Nnaji ya riga ya karyata zargin jabun takardar shaidar karatu da aka yi masa, inda ya nemi hukumar jami’ar da ta saki takardar shaidar karatunsa.

A yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin, ministan ya bayyana cewa zargin jabun takarda na da tushe na siyasa, kuma an tsara shi ne da nufin bata masa suna kafin zaben gwamna na 2027 a jiharsa.

A halin yanzu, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsara ranar 10 ga Nuwamba domin sauraron karar da Minista Nnaji ya shigar kan Jami’ar UNN.

Ministan ya shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1909/2025 ne sakamakon zargin jabun takardar shaida da aka yi masa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC October 10, 2025 Labarai Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe October 10, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: takardar shaidar bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.

 

A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.

 

Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.

 

Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.

 

Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar

A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.

Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu

Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho October 10, 2025 Tattalin Arziki An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi  October 10, 2025 Tattalin Arziki Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole
  • Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya