Obasanjo Ya Kaddamar da Cibiyar Taro Ta Duniya Ta Ahmadu Bello A Bauchi.
Published: 9th, October 2025 GMT
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya kaddamar da sabuwar cibiyar taro ta Ahmadu Bello da aka gina a Bauchi, inda ya bayyana ta a matsayin alamar ci gaba a gwamnatin Gwamna Bala Mohammed.
Da yake jawabi a wajen taron, Obasanjo ya jaddada muhimmancin dunkulewar duniya, inda ya ce babu wata al’umma da za ta iya rayuwa a ware ba tare da yin hulda mai ma’ana da sauran kasashen duniya ba.
Ya yaba wa Gwamna Bala Mohammed bisa ayyukan raya kasa, musamman a fannin samar da ababen more rayuwa, wanda a cewarsa hakan zai karawa Bauchi damar karbar bakuncin taron kasa da kasa da kuma jawo hankalin masu zuba jari.
Tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa irin wadannan wurare na inganta hadin kai da bunkasar tattalin arziki, inda ya kara da cewa dole ne Najeriya ta ci gaba da sanya kanta a matsayin mai shiga tsakani a harkokin duniya.
Gwamna Bala Mohammed ya nuna jin dadinsa ga goyon bayan Obasanjo, inda ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ta ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukan da za su bunkasa ilimi, yawon bude ido, da ci gaban tattalin arziki a fadin jihar.
Sannan ya bayyana cewa Cibiyar Taro ta kasa da kasa ta Ahmadu Bello ta tsaya a matsayin shaida kan manufofin gwamnatinsa na mayar da Bauchi cibiyar tattaunawa, kirkire-kirkire, da zuba jari a Arewacin Najeriya.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa, cibiyar za ta kasance cibiyar hada-hadar kudi ta gida da waje, da suka hada da taron ilimi, taron kasuwanci, da nune-nunen al’adu.
Cov/Alhassan
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cibiyar Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya ASUU a ranar Lahadi ta sanar da shiga yajin aiki na makonni biyu, wanda zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, a duka jami’o’in gwamnati na ƙasar.
Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.
Asuu ta ce yajin aikin na gargaɗi ne bayan cikar wa’adin da suka bai wa gwamnatin Najeriya a watan Satumban da ya gabata.
“Yajin aikin gargadin zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, kamar yadda aka amince a taron NEC na ƙarshe,” kamar yadda Piwuna ya bayyana.
RN