Obasanjo Ya Kaddamar da Cibiyar Taro Ta Duniya Ta Ahmadu Bello A Bauchi.
Published: 9th, October 2025 GMT
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya kaddamar da sabuwar cibiyar taro ta Ahmadu Bello da aka gina a Bauchi, inda ya bayyana ta a matsayin alamar ci gaba a gwamnatin Gwamna Bala Mohammed.
Da yake jawabi a wajen taron, Obasanjo ya jaddada muhimmancin dunkulewar duniya, inda ya ce babu wata al’umma da za ta iya rayuwa a ware ba tare da yin hulda mai ma’ana da sauran kasashen duniya ba.
Ya yaba wa Gwamna Bala Mohammed bisa ayyukan raya kasa, musamman a fannin samar da ababen more rayuwa, wanda a cewarsa hakan zai karawa Bauchi damar karbar bakuncin taron kasa da kasa da kuma jawo hankalin masu zuba jari.
Tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa irin wadannan wurare na inganta hadin kai da bunkasar tattalin arziki, inda ya kara da cewa dole ne Najeriya ta ci gaba da sanya kanta a matsayin mai shiga tsakani a harkokin duniya.
Gwamna Bala Mohammed ya nuna jin dadinsa ga goyon bayan Obasanjo, inda ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ta ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukan da za su bunkasa ilimi, yawon bude ido, da ci gaban tattalin arziki a fadin jihar.
Sannan ya bayyana cewa Cibiyar Taro ta kasa da kasa ta Ahmadu Bello ta tsaya a matsayin shaida kan manufofin gwamnatinsa na mayar da Bauchi cibiyar tattaunawa, kirkire-kirkire, da zuba jari a Arewacin Najeriya.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa, cibiyar za ta kasance cibiyar hada-hadar kudi ta gida da waje, da suka hada da taron ilimi, taron kasuwanci, da nune-nunen al’adu.
Cov/Alhassan
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cibiyar Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi labarin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi cikin alhini da jimami.
Fitaccen malamin da ke Bauchi ya rasu ne a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2026, yana da shekaru 101.
Shugaban Ƙasan ya yi jimamin rasuwar jagoran Darikar Tijjaniyya, yana bayyana shi a matsayin ginshiƙin ɗabi’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa da wa’azi.
Shugaba Tinubu ya ce rashinsa babban rashi ne ba ga iyalansa da dimbin mabiyansa kaɗai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.
Shugaban Ƙasa ya tuna da albarka da goyon bayan da ya samu daga marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a lokacin yakin zaɓen 2023.
“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba, mai cike da natsuwa da hikima. A matsayinaa na mai wa’azi kuma masani kan tafsirin Alƙur’ani Mai Girma, yana da’awar zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.
Shugaba Tinubu ya yi ta’aziyya ga mabiyan Shehun a ci da wajen ƙasa bisa wannan babban rashi.
Haka kuma ya ja hankalinsu da su girmama sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, ƙarfafa dangantakarsu da Allah, da kuma kasancewa masu taushin zuciya ga jama’a.