Aminiya:
2025-11-27@21:15:37 GMT

Sauye-sauyen Tinubu ba su rage talauci a Najeriya ba — Bankin Duniya

Published: 9th, October 2025 GMT

Bankin Duniya ya ce har yanzu talauci na ci gaba da yaɗuwa a Najeriya duk da sauye-sauyen tattalin arziƙi da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar domin daidaita tattalin arziƙin ƙasar.

A wajen ƙaddamar da rahoton ci gaban da aka samu a Abuja, Daraktan Bankin Duniya a Najeriya, Mathew Verghis, ya bayyana cewa aƙalla mutum miliyan 139 ne ke rayuwa cikin ƙangin talauci a shekarar 2025.

Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata rahoton Bankin Duniya kan yawan talakawa a Najeriya NAJERIYA A YAU: Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Nada Shugaban Hukumar Zabe

Ya ce duk da cewa tattalin arziƙin Najeriya ya ɗan bunƙasa, kuma gwamnati tana samun ƙarin kuɗaɗen shiga, yawancin jama’a har yanzu na fama da tsadar rayuwa da wahalhalu.

“Duk da waɗannan nasarorin, yawancin ‘yan Najeriya har yanzu suna cikin wahala. Ƙalubalen da ake fuskanta a yanzu shi ne yadda za a sauya waɗannan nasarorin zuwa inganta rayuwar kowa,” in ji Verghis.

A gefe guda, bankin ya yaba wa Najeriya bisa ƙoƙarin da ta yi wajen daidaita farashin musayar kuɗaɗen waje da rage giɓin kasafin kuɗi.

Sai dai ya ce waɗannan nasarori ba su kawo sauƙi ga rayuwar jama’a ba.

Ya shawarci gwamnati ta rage hauhawar farashin kayan abinci, ta yi amfani da kuɗaɗen jama’a yadda ya kamata, kuma ta faɗaɗa shirin tallafa wa marasa ƙarfi.

Rahoton, ya yi hasashen cewa tattalin arziƙin Najeriya zai iya bunƙasa zuwa 4.4 cikin ɗari nan da shekarar 2027, ta hanyar bunƙasar noma, da masana’antun da ba su da alaƙa da harkar man fetur.

Amma ya yi gargaɗin cewa hauhawar farashin kaya da abinci na iya kawo wa waɗannan nasarori naƙaso.

Ci gaban ba ya shafar talakawa — Masana

Masanin tattalin arziƙi Farfesa Uche Uwaleke, ya bayyana rahoton a matsayin gargaɗi, inda ya ce ci gaban da ake gani bai inganta rayuwar jama’a ba.

Ya buƙaci gwamnati ta zuba jari a noma da masana’antu domin samar da ayyukan yi da rage talauci.

Wani masanin tattalin arziƙi daga Jami’ar Al-Hikmah, Dokta Omotayo Lawal, ya ce ci gaban tattalin arziƙin Najeriya “ba daidaita ba,” domin fa’idar sauye-sauyen ba ta kai ga talakawa ba.

Ya ɗora alhakin hakan kan hauhawar farashi da kuma rashin daidaita manufofi a tsakanin gwamnatoci daban-daban.

“Idan farashi yana hauhaws kuma samun mutane yana raguwa, to babu wata manufa da za a ce tana aiki yadda ya kamata,” in ji Lawal.

Ya jaddada cewa kamata ya yi gwamnati ta mayar da hankali wajen daidaita farashin kayayyaki da inganta samar da abinci.

Ƙungiyar Afenifere ta soki kalaman gwamnatin tarayya

Ƙungiyar Afenifere ta yankin Yarbawa ta soki iƙirarin gwamnatin Tinubu na cewa tattalin arziki ya samu tagomashi, inda ta kira hakan da “ƙarya a kafafen watsa labarai ”

Ƙungiyar ta ce cire tallafin mai da rage darajar Naira sun durƙusar da kasuwanci da jefa miliyoyin mutane cikin ƙangin talauci.

“Yayin da mutane ’yan kaɗan ke amfana, samun mutane ya ragu saboda hauhawar farashi da saukar darajar Naira,” in ji Afenifere a wata sanarwa.

Jama’a na ci gaba da shan wahala

Jama’a da dama sun tofa albarkacin bakinsu, inda suka ce har yanzu sauƙin rayuwa bai samu ba duk da an ce tattalin arziƙi yana farfaɗowa.

Wani mazaunin Jihar Kano, Hamza Bunkure, ya ce: “Mutane har yanzu suna sha wahala wajen siyan abinci. Wutar lantarki ba ta daidaita, kuma man fetur ya yi tsada.”

Wani mai suna Ibrahim Rufai, ya ce farashin kayan abinci ya fara sauka saboda gwamnati ta sassauta dokar hana shigo da abinci daga waje, amma ya nuna damuwa cewa hakan zai iya cutar da manoma.

Ya buƙaci gwamnati ta sayi amfanin gona daga hannun manoma don ƙarfafa musu gwiwa.

Shi kuwa Babatunde Rahman ya buƙaci ake kwatanta gaskiya da amana a tsakanin gwamnati da jama’a domin samun ci gaba mai ɗorewa.

“Har sai an samu adalci, gaskiya, da hangen nesa a tsakanin shugabanni da jama’a, sannan za a samu daidaiton tattalin arziƙi,” in ji Rahman.

Masana sun jaddada cewa duk da cewa Najeriya ta samu ci gaba a fannin daidaita tattalin arziƙi, akwai sauran aiki domin tabbatar da cewa fa’idar ci gaban ta shafi kowa ba wasu tsirarun mutane kawai ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bankin Duniya Hauhawar Farashi Kayan abinci Talakawa Tattalin Arziƙi tattalin arziƙin tattalin arziƙi Bankin Duniya gwamnati ta

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau

Majalisar Wakilai a ranar Alhamis, ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta yi amfani da diflomasiyya da duk wasu hanyoyi don tabbatar da dawowar tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan lafiya daga Guinea Bissau, bayan juyin mulkin sojoji a ƙasar. 

Wannan kuduri ya biyo bayan amincewa da kudurin gaggawa da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar, Farfesa Julius Ihonvbere, ya gabatar.

Ihonvbere ya shaida wa Majalisar cewa Jonathan, wanda ya je ƙasar domin sa ido kan zaɓe, ya makale bayan juyin mulkin, yana mai cewa gwamnati ta nemo hanyoyin da za su tabbatar da dawowarsa lafiya.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza