Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@13:41:39 GMT

Gwamnan Kwara Ya Yabawa Shugaba Tinubu

Published: 9th, October 2025 GMT

Gwamnan Kwara Ya Yabawa Shugaba Tinubu

Gwamna AbdulRazaq ya yabawa Shugaba Tinubu yayin da Sojoji suka tura cikakken birgediya domin fatattakar masu garkuwa da mutane daga dazukan Kwara.

 

 

Hedkwatar sojojin Najeriya ta aika da  cikakken birgediya da manyan kayan aiki a sassa daban-daban na Kwara ta Kudu, domin rage matsalolin tsaro a yankin.

 

Wata sanarwa da sakataren yada labarai gwamnan, Rafiu Ajakaye ya fitar ta ce Tuni dai sojojin suka yi ta luguden wuta ta cikin kauyukan Oke Ode da Babanla, dukkansu a karamar hukumar Ifelodun.

 

Har ila yau, rundunar ta kara da cewa, aikin ya zarce zuwa Edu da Patigi domin ratsa dazuzzukan da masu garkuwa da mutane suka fara kai hare-hare na matsorata a kan al’ummomi daban-daban tare da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 

Ta ce Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, ya gana da Shugaba Bola Tinubu a ziyarar da ya kai a Jos.

 

Ta yabawa shugaban kasa bisa wannan goyon baya, da kuma babban hafsan soji da jami’an tsaro na hadin gwiwa bisa sabon matakin kawar da duk wata barazana ga lafiyar jama’a a jihar.

 

A kwanakin baya ne hedkwatar rundunar ta umarci babban hafsan sojin kasa na GOC 2 Manjo Janar CR Nnebeife da ya koma Kwara domin gudanar da ayyukan dawo da zaman lafiya a yankin.

 

Ya kuma yabawa ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, babban hafsan soji, babban hafsan soji na 2, da duk wani jami’in tsaro.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sojoji Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

An wallafa wasu kundi 2 masu kunshe da ra’ayoyin shugaba Xi Jinping na kasar Sin kan batutuwan da suka shafi mata da yara da kungiyar mata ta kasar, da kuma ra’ayoyinsa kan karfafa zumunci da akidu da al’adun iyali, cikin harsunan Rashanci da Faransanci da Spaniyanci da Larabci, bayan irinsu da aka wallafa cikin harsunan Ingilishi.

 

Madabba’ar tattara bayanai da fassara ta kwamitin tsakiyar JKS ce ta wallafa kundin, wadanda ake sa ran za su taimakawa masu karatu na kasa da kasa kara fahimtar ra’ayoyin shugaba Xi da dabaru da shawarwarin da Sin ta gabatar game da daukaka daidaiton jinsi da raya dukkan harkokin da suka shafi mata a fadin duniya. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace October 12, 2025 Daga Birnin Sin Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan October 12, 2025 Daga Birnin Sin Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno