Fadar Shugaban Ƙasa ta yi fatali da sabon rahoton tattalin arziki da Bankin Duniya ya fitar, wanda ya kiyasta cewa mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci.

Fadar ta bayyana adadin a matsayin wanda ya saba da zahiri kuma ya kauce wa hakikanin halin tattalin arzikin ƙasar.

SSANU da NASU za su yi wa gwamnati zanga-zanga kan rashin cika musu alƙawari 2027: Atiku, Jonathan da Obi ba za su iya kayar da Tinubu ba — Kalu

Mai ba Shugaban Najeriya Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai da sadarwa, Sunday Dare, ya bayyana a shafinsa na X a ranar Laraba cewa dole ne a rahoton bai duba yanayin tsarin auna talauci na duniya ba.

“Duk da cewa Najeriya na daraja haɗin alakarta da Bankin Duniya kuma tana godiya da gudummawar da yake bayarwa wajen nazarin manufofi, adadin da aka ambata dole ne a duba shi cikin daidaitaccen yanayi. Bai dace da gaskiya ba,” in ji Dare.

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa adadin miliyan 139 ya samo asali ne daga layin talauci na duniya na dala $2.15 a kowace rana ga mutum ɗaya, wanda aka kafa a shekarar 2017 bisa tsarin da ake kira karfin iya sayen kayayyaki (PPP), kuma ba za a ɗauke shi a matsayin adadin da ke nuna yawan talakawan Najeriya kai tsaye ba.

Gwamnatin ta ce idan aka fassara wannan adadi zuwa naira bisa farashin musayar kuɗi na yanzu, dala $2.15 a rana na nufin kusan naira 100,000 a wata, wanda ya fi sabon mafi ƙarancin albashi na Najeriya na naira 70,000.

Rahoton ya ƙara da cewa tsarin PPP na amfani da bayanan tarihi na amfani da kaya (inda ƙididdigar ƙarshe a Najeriya ta kasance a shekarar 2018/2019), kuma sau da yawa yakan yi watsi da tattalin arzikin kasar na bayan fage da na dogaro da kai da ke tallafawa miliyoyin gidaje a ƙasar.

Gwamnati ta ce wannan adadi na bankin ƙididdigar duniya ce ta ƙiyasi, ba wai hakikanin yanayin rayuwa a shekarar 2025 ba.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma bayyana cewa gwamnatin yanzu ta faɗaɗa shirye-shiryen jin ƙai da tallafi da dama don rage tasirin gyare-gyaren da aka yi kwanan nan, tare da shimfiɗa tubalin bunƙasa kasa mai ɗorewa a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bankin Duniya Fadar Shugaban Ƙasa ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

 

Ya ce barazanar kakaba karin haraji ba hanya ce da ta dace ta hulda da Sin ba, yana mai nanata cewa, kasar Sin ba ta sauya matsayarta kan batun yakin cinikayya ba, wato ba ta son hakan, amma kuma ba ta tsoro. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje October 12, 2025 Daga Birnin Sin Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace October 12, 2025 Daga Birnin Sin Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya