Aminiya:
2025-10-13@13:34:42 GMT

An kashe ɗan shekara 13 da shanu 36 a wani sabon hari a Filato

Published: 8th, October 2025 GMT

An kashe wani yaro ɗan shekara 13 mai suna Abubakar Wada da shanu 36, yayin da wasu ’yan bindiga sun kai wa makiyaya hari a kusa da ƙauyen Inzon da ke yankin Fan, a Ƙaramar Hukumar Barkin Ladi a Jihar Filato.

Aƙalla shanu 49 kuma sun ɓace ba tare da sanin inda suka shiga ba.

’Yan sanda sun kama ɗan bindiga a kan iyakar Najeriya da Kamaru Kamfanonin rarraba lantarki sun tafka asarar biliyan 358 a cikin wata uku – NERC

Shugaban ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN), a Jihar Filato, Ibrahim Yusuf Babayo, ya bayyana cewa harin ya faru ne da yammacin ranar Talata lokacin da wasu makiyaya uku ke dawowa daga kiwo.

Ya ce ’yan bindigar sun buɗe wa dabbobin wuta, tare da kashe yaron wanda makiyayi ne, yayin da sauran biyun suka tsallake rijiya da baya.

Babayo ya ce: “Mun yi asarar sama da shanu 80, saboda 36 an kashe su, yayin da 49 suka ɓace. Mun gano cewa maharan Berom ne daga yankin Fan.

“Wannan abu ne mai ban tsoro da rashin imani. Makiyayan suna tafiya lafiya ba tare da sun tayar da hankali ba.”

Ya buƙaci makiyaya a faɗin jihar su kwantar da hankalinsu, su bar jami’an tsaro su gudanar da bincike, inda ya yi gargaɗin ɗaukar doka a hannu.

Sakataren MACBAN a Barkin Ladi ya tabbatar da cewa dukkanin hukumomin tsaro sun samu rahoton harin, inda jami’an Operation Enduring Peace, DPO na Barkin Ladi suka ziyarci wajen da harin ya auku.

Ya ƙara da cewa a ranar Lahadin da ta gabata, an kashe shanu guda biyar a wannan yankin kuma matasan Berom ake zargi.

Matasan Berom sun musanta zargin

Shugaban ƙungiyar matasan Berom (BYM), Barista Solomon Dalyop, ya musanta zargin, inda ya bayyana cewa mutanen Berom masu ƙauanar zaman lafiya ne.

Ya ce: “Waɗannan zarge-zargen kawai wata hanya ce ta neman dalilin kai wa mutanenmu hari.

“A gaskiya, an kai hare-hare guda biyu ta hannun wasu da ake zargin Fulani ne a ranar 6 ga watan Oktoba, 2025 da misalin ƙarfe 7:30 na yamma, inda aka kashe wani mutum mai suna Timothy Ishaku Chollom.”

Dalyop, ya ƙara da cewa ci gaba da kiwo a gonaki da wuraren zama yana tayar da hankali, kuma yana barazana ga rayuka a yankin Fan.

Sojoji sun fara bincike

Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojojin Najeriya Sashe na 3, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya ce rundunar sojin ta fara bincike kan lamarin.

Ya ƙara da cewa sun tuntuɓi kwamandan sashen da ke yankin domin tabbatar da bayanai game da harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Makiyaya zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Bugu da kari, an rufe shafukan hakar ma’adanai haramtacce 98 a fadin kasar.

 

“An kiyasta cewa Nijeriya na asarar kusan Dala biliyan 9 a kowace shekara sakamakon haramtacciyar hakar ma’adanai. Wannan sata ta albarkatunmu da ya kamata ta bunkasa kasarmu ta wuce kima, kuma lokaci ya yi da za a kawo karshensa,” in ji Abdulraheem.

 

A cewar sa, kwamitin na da alhakin hana asarar kudaden shiga, tabbatar da gaskiya da adalci a harkokin hakar ma’adanai, da tabbatar da cewa dukiyoyin ma’adanin kasar suna ba da cikakken gudunmawa ga ci gaban tattalin arziki.

 

“Yayin da muke ci gaba, daya daga cikin manyan manufofin wannan kwamitin shi ne hana asarar kudaden shiga da haramtacciyar hakar ma’adanai da ayyukanta ke haifarwa, wanda ba wai kawai ke satar kudaden asusun kasa ba, har ma yana hana bunkasar ayyukan hakar ma’adanai na halal wadanda za su iya ba da gudunmawa mai yawa ga cikakken kudin shiga na cikin gida na kasa (IGR).

 

“Ta hanyar tsauraran kulawa da tsare-tsare, za mu karfafa hanyoyin bibiyar kudaden shiga kuma mu tabbatar cewa duk fa’idojin da ke tattare da bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya sun shiga asusun gwamnati kai tsaye, ba tare da a sata ta hanyar haramtacciyar hakar ma’adanai ba.

 

“Haka kuma, batun laifuka da lalacewar muhalli da ke da alaka da haramtacciyar hakar ma’adanai yana da muhimmanci. Wadannan ayyuka ba kawai suna kara rashin tsaro ba ne, har ma suna haifar da gurbatar hanyoyin ruwa, lalata dazuzzukanmu, da tilasta kwashe al’ummomi masu rauni daga gidajensu. Wannan lamari ne na gaggawa na kasa wanda ya zama dole a tunkare shi kai tsaye,” in ji shi kari.

Yana mai jaddada cewa majalisar kasa za ta yi duk mai yiwuwa ba tare da wasa ba, ya ce kwamitin yana tsaye kafada da kafada kan ikonsa na kundin tsarin mulki da ‘yan Nijeriya suka ba shi.

Yayin da yake tabbatar da shirin majalisar wajen daukar mataki mai karfi kan duk wanda aka same shi da hannu a haramtacciyar hakar ma’adanai, Shugaban Kwamitin ya yi kira ga ‘yan kasa da su bayyana masu laifi a cikin al’ummominsu don amfanin kasa baki daya.

“Mun kuduri aniyar cika wajibcinmu na sa ido kamar yadda kundin tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya ya tanadar, wajen fallasa cin hanci da rashawa a kowace hanya, dakile miyagun ayyuka, da tabbatar da cewa albarkatunmu ana amfani da su ne domin amfanin duk ‘yan Nijeriya.

“Ta hanyar wannan tsauraran sa ido ne za mu kawar da cutar haramtacciyar hakar ma’adanai daga kasarmu, mu kare muhalli, da kuma tabbatar da jin dadin ‘yan kasa. Ta amfani da ikon da aka ba mu, za mu gudanar da bincike, tattara hujjoji, da bayar da shawarwarin da za su dawo da hankali da gaskiya a bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya,” in ji shi kari.

Game da Kamfanin Karafa na Ajaokuta (Ajaokuta Steel Company), ya tabbatar cewa gwamnatin Tinubu ta nuna jagoranci da kuma shirin farfado da wannan dukiyar kasa.

“Tsawon shekaru da dama, Kamfanin Karafa na Ajaokuta ya kasance alamar bai cika burinsa ba. Ko ma dai yaya, ina alfahari da cewa yanzu yana kan hanyar cika ainihin burinsa. Gwamnatin yanzu ta nuna kwazo na siyasa da ba a taba gani ba wajen farfado da wannan muhimmin dukiyar kasa.”

“Wannan yana bayyana ne a cikin nadin wani kwararren dan kasa domin jagorantar farfado da kamfanin, mataki da ke ba mu fata ga makomar masana’antar karfe ta Nijeriya.

Tare da shirye-shiryen Ajaokuta na samun nasara, muna kallon hakan ba kawai a matsayin sauyin tattalin arziki ba, har ma a matsayin ginshiki ga masana’antu, samar da ayyukan yi, da dogon lokacin bunkasar tattalin arziki,” in ji shi.

Wakilin (NSCDC), Kwamandan Ma’aikatan Tsaron Hakar Ma’adanai, Attah Onoja, ya tabbatar wa kwamitin da cikakken hadin kai daga jami’ai.

Onoja ya bayyana cewa tun bayan kaddamar da aikin Mining Marshals a watan Maris 2024, NSCDC ta kama masu hakar ma’adanai haramtacce sama da 500, inda kimanin 270 daga cikinsu ke fuskantar shari’a a halin yanzu.

“Ina so in bayyana cikin gaggawa cewa sama da masu hakar ma’adanai 500 an kama su a lokacin wannan aikin. Kuma daga cikin wannan adadi, kimanin 270 suna fuskantar shari’a a yanzu kamar yadda muke magana a yau.

“Jami’an NSCDC, a matsayin hukuma, tana tabbatar wa wannan Kwamitin girmamawa da cikakken hadin kai da goyon baya a duk inda ya zama dole domin tabbatar da cewa an cimma wannan muhimmin burin tattalin arziki,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Labarai Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN October 10, 2025 Labarai ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno
  • Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara