Muluku ya bayyana hakan ne a ranar Talata a babban birnin jihar Lafiya, yayin wani taron bayar da rahoton ma’aikatu da Kwamishinan Bayanai, Al’adu da Yawon Bude Ido, Dr. Ibrahim Tanko, ya shirya domin bai wa jami’an gwamnati damar bayyana nasarorinsu.

 

Kwamishinan ya ce wannan yunkuri na cikin ƙoƙarin gwamna Sule na inganta samun ruwan sha mai tsafta da haɓaka ci gaban karkara a fadin jihar.

 

Ya bayyana cewa gwamnati ta kuma gyara burtsatse 300 a kauyuka da birane domin rage matsalar ƙarancin ruwa da kuma ƙara wa jama’a damar samun ruwan sha mai tsafta.

 

Muluku ya ƙara da cewa, akwai gidan ruwa fiye da tara (9) a Awe, Obi, Keana, Lafia, Nassarawa-Eggon, Akwanga, Wamba, Nasarawa da Toto, kuma dukkansu gwamnati tana kula da su a halin yanzu.

 

Ya ce gwamnati ta bayar da ayyukan tono da tsaftace gidajen ruwa, tare da shirin gina sababbi domin biyan bukatar sababbin unguwanni da suka taso.

 

Sai dai kwamishinan ya koka da cewa, akwai matsaloli da ke hana samun cikakken ruwan sha mai tsafta, kamar lalata kayan aiki da satar igiyoyin wutar lantarki da famfo daga wasu ɓata-gari.

ShareTweetSendShareMASU ALAKA Manyan LabaraiKwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi October 8, 2025LabaraiABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki October 8, 2025LabaraiGwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu October 8, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya sauka sheƙa daga jam’iyyar SDP zuwa jami’yyar haɗaka ta ADC.

Komawar El-Rufai jam’iyyar ADC a hukumance wani mataki ne da ake ganin zai kawo sabon salo a siyasar adawa wajen ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.

An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos

A wannan Alhamis ɗin ce El-Rufai ya kammala rajistar zama mamba na jam’iyyar ADC a mazaɓarsa ta Unguwar Sarki da ke birnin Kaduna, inda ya yi alƙawarin amfani da jam’iyyar ADC wajen fuskantar abin da ya kira rashin ƙwarewa a jagorancin gwamnatin jihar.

“Ina da cikakkiyar rajista a jam’iyyar African Democratic Congress,” in ji shi a gaban manyan jami’an jam’iyyar, ciki har da Mataimakin Shugaban ADC na Arewa maso Yamma, Jafaru Sani, da Sakataren Yi wa Mambobi Rajistar Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Sadiq Yar’adua.

A watan Maris na bana ne dai El-Rufai ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP a wani yunƙuri na shirya haɗin gwiwar adawa, sai dai ya ce tattaunawar da suke yi a SDP ɗin ta gaza haifar da ɗa mai ido wajen cimma muradinsu saboda “tsoma bakin gwamnati da kuma cin hanci da wasu shugabannin jam’iyyar ke yi.”

Da yake jawabi kan siyasar Jihar Kaduna, El-Rufai ya yi kira ga jama’a da su yi rajista da ADC domin “maimaita abin da muka yi a 2015,” yana mai zargin gwamnatin APC mai ci da sakaci da jagorancin al’umma.

“Ina kira ga dukkan ’yan Kaduna masu shekaru 18 zuwa sama da su fito su yi rajista. Da ikon Allah, zamu sake kawar da gwamnatin da ta nuna gazawa.

“Mu da muka taimaka muka ɗora su a kujerar mulki, za mu taimaka wajen dawo da su gida… kafin su wuce kotu,” in ji El-Rufai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Zanga-Zangar Lumana
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina