Ɓarayin daji sun kashe kwamandan maharba a Kaduna
Published: 5th, October 2025 GMT
Wasu da ake zargin ’yan fashin daji ne sun kashe ɗaya daga cikin kwamandojin maharba a yankin Gangara da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.
Lamarin ya faru ne a yau Asabar, 4 ga watan Oktoba, 2025, inda aka tabbatar da mutuwar Malam Kabiru, wanda yake ɗaya daga cikin kwamandojin ƙungiyar maharba ta ƙasa, reshen Giwa.
Rahoto ya bayyana cewa Malam Kabiru ya rasu ne yayin aikin ceto wasu mutane da ’yan fashi suka sace daga yankin Danja na Jihar Katsina.
Shugaban ƙungiyar maharba ta ƙasa, Kwamanda Usman Taju, ya tabbatar wa Aminiya faruwar lamarin, jim kaɗan bayan jana’izar marigayin.
Ya ce: “Da safiyar Asabar muka samu labarin cewa ’yan fashi sun yi garkuwa da wasu maza da mata daga Danja, suka shigo da su Giwa. Nan take muka haɗu domin ceto su.
“Mun samu nasarar ceto mata uku daga hannun ’yan fashin, amma abin baƙin ciki, ɗaya daga cikinmu, Malam Kabiru Gangara, ya rasa ransa yayin aikin.”
Usman Taju, ya bayyana cewa marigayin ya rasu ne a kan aikin kare rayuka da dukiyar jama’a, inda ya ce hakan babban abin alfahari ne.
Ya roƙi gwamnatin Jihar Kaduna da ta taimaka musu da kayan aiki da horo, domin ci gaba da tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
“Haƙiƙa muna fama da ƙalubale da dama, amma hakan ba zai hana mu ci gaba da kare jama’a ba,” in ji shi.
Kwamandan ya nemi gwamnati ta riƙa kula da iyalan jami’an da suka rasu a bakin aiki, domin hakan zai bai wa sauran maharba ƙwarin guiwa.
Marigayin ya rasu ya bar mata uku da yara shida, kuma an binne shi a ƙauyensu na Gangara, a Jihar Kaduna.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, bai yi nasara ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan fashin daji kwamanda maharba Maharbi Jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana farin cikinsa bisa dawowar ’yan mata 24 da ’yan ta’adda suka sace a Maga, Jihar Kebbi.
’Yan ta’addan sun kai hari makarantar ranar 17 ga wantan Nuwamban 2026, inda suka yi awon gaba da ’yan matan, jim kaɗan bayan wata rundunar soji ta bar harabar makarantar.
Lamarin Kebbi ya haifar da wasu sace-sace makamanta a Eruku da ke Jihar Kwara da kuma Papiri a Jihar Neja.
An sako dukkan mutune 38 da aka sace a Eruku ranar Lahadi, inda a wannan ranar ce shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) Jihar Neja ya ce an samu yara 50 daga cikin ɗaliban makarantar Katolika da suka ɓace a gidajen iyayensu.
Shugaba Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ganin an kubutar da dukkan mutanen da ’yan ta’adda suka sace.
Ya umarci jami’an tsaro da su ƙara ɗaukar matakan gaggawa don ceto sauran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.
“Ina farin cikin cewa an samu dukkan ’yan mata 24. Ya zama wajibi mu ƙara tura jami’an tsaro yankunan da ke da rauni don hana sake faruwar irin wannan lamari. Gwamnatina za ta bayar da dukkan tallafin da ake buƙata don cimma haka,” in ji Shugaba Tinubu.