Aminiya:
2025-10-13@17:47:14 GMT

Hukuma ta fara binciken Ganduje kan zargin karkatar da N4bn a Kano

Published: 5th, October 2025 GMT

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta fara binciken Tsohon Gwamnna Jihar, Abdullahi Umar Ganduje, kan zargin karkatar da sama da Naira biliyan huɗu zuwa aikin Dala Inland Dry Port.

Ana zargin kuɗin an kashe su wajen bayar da kwangila don samar da wasu abubuwan more rayuwa a wajen aikin.

Mata da yara 95,000 ke mutuwa a sanadin shaƙar hayaƙin girki — Uwargidan Fubara Fitaccen ɗan jarida a Kano, Aliyu Abubakar Getso ya rasu

An gano yadda aka mayar da kashi 20 na kuɗin wanda mallakar jihar ne zuwa ga iyalan Ganduje a shekarar 2020.

Wannan ya janyo an cire Jihar Kano daga cikin masu mamallaka kamfanin, inda ’ya’yan Ganduje ke riƙe da muƙamakn daraktoci da wasu masu hannun jari.

Majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa binciken ya fara ne bayan hukumar ta samu koke-koke daga jama’a kan zargin karkatar da kuɗin.

Da yake tabbatar da lamarin, shugaban hukumar PCACC, Saidu Yahya, ya ce binciken zargin karkatar da kuɗin jihar ya kusa kammalawa.

“Eh, mun samu koke-koke daga jama’a kan zargin karkatar da sama da Naira biliyan huɗu na kuɗin Jihar Kano zuwa Dala Inland Dry Port da tsohuwar gwamnatin Gwamna Abdullahi Ganduje ta yi,” in ji Yahya.

“Zuwa yanzu mun gayyaci wasu da ake zargi da hannu a lamarin. An kama mutum ɗaya, an yi masa tambayoyi, daga baya kuma aka sallame bisa beli bayan ya bayar da muhimman bayanai.

“Bincike ya kuma gano cewa ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi yanzu yana Yola, a Jihar Adamawa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za a kai lamarin zuwa kotu nan ba da jimawa ba, domin binciken ya tabbatar da cewa akwai isassun hujojji don ci gaba da shari’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dala Inland Dry Port Karkatar Da Kuɗi zargi kan zargin karkatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine

Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da ta danganta da na karya da Amurka ke yi wa kasar cewa ta na da hannu a yakin da ake yi a Ukraine, tana mai daukar wadannan zarge-zarge a matsayin wani makirci na siyasa da nuna kiyayya.

A cewar ma’aikatar harkokin wajen Cuba, hukumomi “ba su da wani takamaiman bayani kan ‘yan kasar Cuba” da suka shiga ko kuma suke shiga cikin rikicin “da kansu” a cikin “dakarun sojan bangarorin biyu da ke rikici da juna” tsakanin Rasha da Ukraine.

Tsakanin shekarar 2023 zuwa 2025, kotunan kasar Cuba sun saurari kararrakin laifuka tara da suka shafi ayyukan sojan haya, inda suka yanke wa wadanda ake tuhuma 26 hukuncin zaman gidan yari tsakanin shekaru 5 zuwa 14.

Cuba ta kuma fayyace cewa duk wani daukar aiki na ‘yan kasar Cuba don shiga yakin kasashen waje, kungiyoyin waje ne ke aiwatar da su, wanda bai da alaka da gwamnatin Cuba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano
  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka  Rusa A Arewacin Yankin