Fitaccen ɗan jarida a Kano, Aliyu Abubakar Getso ya rasu
Published: 5th, October 2025 GMT
Allah Ya yi wa fitaccen ɗan jarida a Jihar Kano Aliyu Abubakar Getso, rasuwa da safiyar yau Lahadi bayan fama da rashin lafiya.
Abubakar Getso ya yi aiki a kafafen yaɗa labarai da dama da suka haɗar da na gwamnati da kuma masu zaman kansu.
Ya rasu ya bar mata uku da ’ya’ya da jikoki da dama.
Iyalai sun ce za a yi jana’izarsa da misalin karfe 9:30 na safiyar yau Lahadi a gidansa da ke Second Gate a Unguwar Janbulo, Kabuga.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aliyu Abubakar Getso Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta samu nasara a wasan mako na 14 na Nigeria Premier Football League (NPFL), bayan da ta doke Ikorodu City da ci 2–1 a filin wasa na Muhammad Dikko, da ke birnin Katsina.
Wannan ita ce nasara ta uku da Pillars ta samu a kakar bana, cikin wasanninta 14, inda ta yi kunnen doki uku, sannan ta sha kashi shida.
’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun TuraiKafin wannan wasan, Kano Pillars ta yi wasanni takwas a jere ba tare da samun nasara ba.
Pillars ta zura kwallayenta ne ta hannun Rabiu Ali, wanda ya zura ta farko a minti na 3, sai Olakunle Alaka ya kara ta biyu a minti na 30.
A daidai minti na 45, kafin a je hutun rabin lokaci, Joseph Arumala ya rage tazara ga Ikorodu City.
Duk da wannan nasarar, Kano Pillars ta ci gaba da zama a matsayi na 20, inda take da maki 9 a ƙasan teburin gasar.
A wani labarin, ƙungiyar Katsina United ta samu nasarar doke Enyimba da ci 3–2 a birnin Ilorin, inda take buga wasanninta na gida bayan dakatar da ita daga yin wasa a filin gidan ta a Katsina.