Wike ya gana da Fubara da dattawan Ribas kafin kafa sabuwar majalisar zartarwa
Published: 5th, October 2025 GMT
Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya gana da Gwamna Siminalayi Fubara da wasu Dattawan Jihar Ribas.
Mai taimaka wa Wike kan yaɗa labarai, Lere Olayinka ne, ya wallafa hoton ganawar a shafukan sada zumunta, inda ya ce kakakin Majalisar Dokokin jihar, Martin Amaewhule, ya halarci taron.
An yi wata gagarumar zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Turai Ban taɓa cewa Buhari yana da alaƙa da Boko Haram ba — JonathanKo da yake Olayinka bai bayyana abin da aka tattauna a taron ba, amma wannan ce ganawa ta farko da aka yi tsakanin Wike da Fubara tun bayan da gwamnan ya kori wasu daga cikin muƙarrabansa yayin da yake shirin kafa sabuwar majalisar zartarwa a jihar.
Rahotanni sun nuna cewa naɗa sabbin kwamishinoni na daga cikin yarjejeniyar sulhu da Shugaba Bola Tinubu ya yi tsakanin Wike da Fubara lokacin da ake tsaka da rikicin siyasa a jihar.
A yayin wani taron ban kwana da tsofaffin Kwamishinoni a Fadar Gwamnatin jihar da kw Fatakwal a ranar Laraba, Gwamna Fubara ya ce an tilasta masa sallamar muƙarrabansa saboda hukuncin Kotun Ƙoli da ya shafi naɗinsu.
A farkon shekarar nan ne, Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa Majalisar Dokokin da ke goyon bayan Wike ce halastacciya ce.
A lokacin da rikicin siyasar ya yi ƙamari a jihar, wasu daga cikin muƙarraban Fubara sun samu tantancewa daga ɓangaren majalisar da Victor Oko-Jumbo ke jagoranta, amma tsahin Wike bai amince da hakan ba.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Nelson Chukwudi, ya fitar, ya ce Fubara ya gode wa tsofaffin kwamishinonin bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.
Gwamnan, ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai da Shugaba Tinubu wajen gina ƙasa mai cike da zaman lafiya da ci gaba.
Ya ƙara da cewa zai ci gaba da yi wa Jihar Ribas hidima, tare da yi wa ’yan kasa fatan alheri a bikin ranar samum ’yancin kai.
Sanarwar ta ƙara da cewa, dukkanin kwamishinoni da jami’an gwamnati da hukuncin Kotun Ƙoli ya shafa, an sallame su daga muƙamansu nan take.
Bayan ƙarewar dokar ta-ɓaci, ’yan majalisar jihar, sun buƙaci Gwamna Fubara da ya miƙa sunayen sabbin kwamishinoni.
Ana sa ran gwamnan zai kafa sabuwar majalisar zartarwa nan ba da jimawa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fubara Kwamishinoni Majalisar Zartarwa
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
Shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutum uku zuwa Majalisar Dattawa, domin tantance su a matsayin sabbin jakadan Najeriya.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne, ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Laraba.
Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a KadunaWaɗanda aka zaɓa su haɗa da Kayode Are daga Jihar Ogun, Aminu Dalhatu daga Jihar Jigawa da kuma Ayodele Oke.
Bayan karanta takardar Tinubu, Akpabio ya ce, “Sunaye uku ne zuwa yanzu, tabbas sauran za su biyo baya.”
Tun bayan ɗarewarsa kan mulki a 2023, Tinubu bai naɗa jakadu ba har yanzu.
Mutane da dama sun daɗe suna ƙorafin kan jinkirin naɗa jakadun.
Amma wasu na ganin aike sunayen jakadun na da alaƙa da barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na ɗaukar matakin soji a kan Najeriya, kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.
A wata hira da aka yi da shi a watan Satumba, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce babu wata matsala game da jinkirin.
Ya ce, “Dukkanin ofisoshin jakadancinmu suna aiki yadda ya kamata. Kowace ofishi yana gudanar da ayyukansa yadda ya dace. Rashin jakadu ba zai haifar da giɓi ba.”
Ya ƙara da cewa duk da cewa jakada shi ne shugaban ofishin jakadanci, akwai kwamishinoni, wakilai da ma’aikatan diflomasiyya da ke tafiyar da harkokin yau da kullum.
A cewarsa, “Diflomasiyya ba aikin mutum ɗaya ba ne. Tsarin ya tanadi irin wannan yanayi.”
Tuggar, ya kuma ce shugaban ƙasa ne kaɗai ke da ikon naɗa jakadu, kuma zai yi hakan a lokacin da ya dace.
Ya bayyana cewa, “Shugaban ƙasa yana duba batun, kuma za a sanar da sunayen a lokacin da ya dace.”
Ya ƙara da cewa, “’Yan Najeriya a ƙasashen waje har yanzu suna samun ayyuka, kuma mu’amala da ƙasashen da muke hulɗa da su ba ta ragu ba.”
Ya ce kuma akwai ƙasashe da dama da suka shafe dogon lokaci ba tare da jakadu ba, amma hakan bai lalata dangantakarsu da wasu ƙasashe ba.
Ya ce, “Wannan ba sabon abu ba ne. Diflomasiyya tana da tanadin irin wannan yanayi. Abin da ya fi muhimmanci shi ne aiki, ba kwaikwayo ba.”
A ƙarshe ya ce Najeriya tana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran ƙasashen duniya.
“Manufofin ƙasashen waje na Najeriya sun bayyana, kuma ana jinmu a duniya. Abin da muke yi shi ne tabbatar da cewa ofisoshinmu suna samar da sakamako mai amfani ga ’yan Najeriya.”