Gwamna Namadi ya raba wa mata 1,400 tallafin kayan ɗinkin hula a Jigawa
Published: 4th, October 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya ƙaddamar da shirin tallafa wa mata 1,400 da kayan sana’ar ɗinkin hula domin bunƙasa harkokin kasuwancinsu.
A wajen bikin raba kayan, Gwamna Namadi ya ce ɗinkin hula tsohuwar sana’a ce da mata suka gad tun daga iyaye da kakanni, wadda ke taimaka musu wajen dogaro da kai da kuma kula da iyalansu.
Waɗanda suka ci gajiyar wannan shiri na farko, sun fito daga ƙananan hukumomi bakwai na masarautar Dutse, waɗanda suka haɗa da Dutse, Kyawa, Birnin Kudu, Buji, Gwaram, Jahun da Miga.
Gwamnan ya ce da kayan aikin da aka ba su, mace za ta iya ninka yawan hulunan da ta ke ɗinkawa cikin ƙanƙanin lokaci, wanda hakan zai ƙara mata samun kuɗaɗe da zaman lafiya a cikin gida.
Ya ƙara da cewa wannan shiri matakin farko ne na manufar gwamnatinsa na bunƙasa sana’o’in gargajiya zuwa masana’antu masu inganci nan gaba, inda ƙananan sana’o’i za su iya girma su koma manyan masana’antu.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin, a madadin ragowar matan, Hajara Sani, ta ce wannan tallafi zai taimaka musu sosai.
“Muna gode wa Gwamnan kan wannan tallafi. Tabbas za mu yi amfani da kayan yadda ya ce saboda kowa a nan yana murna. Kuma za mu bai wa mara ɗa kunya da yardar Allah,” in ji ta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Namadi Jigawa Kayan Ɗinki
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
An sake tabbatar wa ma’aikatan Gwamnatin Tarayya FG da suka yi ritaya cewa za a biya su wani bangare na kudaden ariyas a cikin wannan watan, kamar yadda hukumomin da abin ya shafa suka yi alkawari.
Mataimakin Sakataren ƙungiyar masu karɓar fansho ta ƙasa, Alhaji Ahmed Gazali, ya bayar da wannan tabbaci yayin da ake tattaunawa da shi ta wayar tarho daga Abuja.
Alh. Ahmed Gazali, ya yi bayanin cewas daraktan dake kula da kudade na ofishin akanta janar na tarayya ya tabbatar da daukan matakin hakan na biyan kudaden.
Ya bayyana fatan ganin kudirin FG na gaggauta biyan kudade, domin dakatar da duk wata zanga zanga wanda hakan bai dace ba ga ma’aikatan da suka yi ritaya domin bata martaban kasan nan.
Hakan kuma masu karban fensho a Radion Tarayya na kasa FRCN da Gidan talabijin na kasa NTA dake Kaduna sun nuna damuwarsu game da zargin da ake yi cewa ana kokarin wulakanta shugabannin kungiyar ma’aikatan da suka yi ritaya karkashin jagorancin kwamaret Munkaila Ogunbote.
DAGA SULEIMAN KAURA