Aminiya:
2025-10-13@15:50:21 GMT

Gwamna Namadi ya raba wa mata 1,400 tallafin kayan ɗinkin hula a Jigawa

Published: 4th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya ƙaddamar da shirin tallafa wa mata 1,400 da kayan sana’ar ɗinkin hula domin bunƙasa harkokin kasuwancinsu.

A wajen bikin raba kayan, Gwamna Namadi ya ce ɗinkin hula tsohuwar sana’a ce da mata suka gad tun daga iyaye da kakanni, wadda ke taimaka musu wajen dogaro da kai da kuma kula da iyalansu.

’Yan sanda sun bindige Lakurawa 3 har lahira a Kebbi Dalilin da ya sa na tsere Kamaru bayan Boko Haram ta ƙone fadata a Borno — Basarake

Waɗanda suka ci gajiyar wannan shiri na farko, sun fito daga ƙananan hukumomi bakwai na masarautar Dutse, waɗanda suka haɗa da Dutse, Kyawa, Birnin Kudu, Buji, Gwaram, Jahun da Miga.

Gwamnan ya ce da kayan aikin da aka ba su, mace za ta iya ninka yawan hulunan da ta ke ɗinkawa cikin ƙanƙanin lokaci, wanda hakan zai ƙara mata samun kuɗaɗe da zaman lafiya a cikin gida.

Ya ƙara da cewa wannan shiri matakin farko ne na manufar gwamnatinsa na bunƙasa sana’o’in gargajiya zuwa masana’antu masu inganci nan gaba, inda ƙananan sana’o’i za su iya girma su koma manyan masana’antu.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin, a madadin ragowar matan, Hajara Sani, ta ce wannan tallafi zai taimaka musu sosai.

“Muna gode wa Gwamnan kan wannan tallafi. Tabbas za mu yi amfani da kayan yadda ya ce saboda kowa a nan yana murna. Kuma za mu bai wa mara ɗa kunya da yardar Allah,” in ji ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Namadi Jigawa Kayan Ɗinki

এছাড়াও পড়ুন:

Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja

Wani soja mai muƙamin Las Kofur ya ɗirka wa matarsa harbi har lahira sannan ya kashe kansa a Jihar Neja.

Las Kofur Akenleye Femi da ke aiki a Bataliya ta 221, ya yi wannan aika-aika ne a Barikin Sojoji na Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja.

Muƙaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Soja ta 22 da ke Ilorin, Kyaftin Stephen Nwankwo, ne ya tabbatar da lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce abin ya faru ne a ranar 11 ga Oktoba, 2025.

Ya ce mutuwar sojan da matarsa ta haifar da tashin hankali a cikin sansanin soja, inda mazauna wurin suka shiga ɗimuwa da mamaki kan abin da zai iya jawo irin wannan lamari.

Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako

“An gano gawar Last Kofur Femi da matarsa ne a cikin dakinsu da ke Block 15, Room 24 na Corporals and Below Quarters a Wawa Cantonment,” in ji Kyaftin Nwankwo.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa sojan yana kan aiki a cikin sansanin kafin ya nemi izinin zuwa gida domin wasu bukatun kansa, sai daga bisani aka gano gawarsu a gida.

Kyaftin Nwankwo ya ce an ajiye gawar mamatan domin ci gaba da bincike, kuma rundunar sojan na aiki tukuru don gano musabbabin lamarin.

Rundunar Soja ta Najeriya ta bayyana matuƙar baƙin cikinta kan wannan abin takaici, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalai, abokai da abokan aikin mamatan.

Kwamandan Rundunar, Birgediya Janar Ezra Barkins, ya sha alwashin gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru, tare da ɗaukar matakan da za su hana faruwar irin haka a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida