An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana
Published: 4th, October 2025 GMT
Ana ta rade-radin an baki sarauta, shin mene ne gaskiyar maganar?
Alhamdulillah, maganar an bawa Zahra’u sarauta ba karya ba ne, hakkun haka ne an ba ni sarauta.
Mutane za su so su ji, shin daman Haj. Zahra’u ‘yar Ghana ce, tana da sarauta a Ghana?
A’a! Ni ba ‘yar Ghana ba ce, ba abin da na hada da Ghana, sai dai so da yarda, saboda ma’abota kallon finafinan hausa ne.
Me ya sa aka baki sarauta?
An ba ni wannan sarauta ne ba dan na gada ba, an ba ni ne a matsayin cancanta, da so da yarda da amincewa a birnin Kumasi da Accra. Na ziyarci wadannan masarautu domin karrama su da basu allon girma wato ‘Award’. Na je na gaishe su, na ziyarce su, ubangiji Allah ya sa suka ce da ni to, wannan sarki na Kumasi ya ce da ni,shi fa ba zai iya yi min komai ba sai dai ya ba ni Jakadiyarsa ta London da America, da nan Kumasi da kuma Najeriya. Haka zalika shi kuma sarkin Accra ya ba ni magajiyarsa ta London da America da Accra da kuma nan Najeriya. Alhamdulillah kuma na gode, an karrama ni kuma na ji dadi.
Me ya fi burge ki a nadin sarautar da aka yi miki?
To, Alhamdulillah ita dai wannan sarauta, sarauta ce me dadi, an ba ni kudi sannan kuma an yi min albashi. Sannan ga alfarma, alfarmar da aka yi min idan za a fita kamar turai wajen London zuwa America an ba ni alfarmar mutum uku ni ta hudu. Za a ba ni kujera mu je mu dawo duk abin da za a yi. Sannan alfarma ta biyu idan a Ghana za a yi taro an ba ni alfarmar mutum goma sha daya ni ta sha biyu, za a ba ni kujera mu je mu dawo. Dan haka wannan abun alfahari ne a gare ni.
Wane irin farin ciki ki ke ji game da wannan sarauta da aka baki?
Gaskiya na ji dadi kwarai da gaske, kuma na yi wa Allah godiya. Dan ban taba tsammanin zan taka wannan mataki ba, wanda Allah ya sa ina da rabon shi. Kuma na taka shi, komai nufin Allah ne. Mutanen Ghana sun nunan tamkar uwa daya uba daya, an karramani an mutuntani an daukake ni, ina alfahari da mutanen Ghana, sun ba ni tarihin da ba zan taba mantawa da shi a rayuwata ba.
Ko akwai wani abu da ki ke son fada wanda baki fade shi ba, game da wannan sarauta?
Ina mika sakon godiya musamman ga mai girma Alh. Ahmed Ibrahim Watara, shi ne sarkin Wangarawan Kumasi Allah ya kara masa lafiya, shi ya fara ba ni wannan mikami na Jakadiya. Shi kuma Alhaji Yahaya Hamisu Bako maimartaba (Sarkin Zangon Accra), Ghana shi kuma ya ba ni magajiya. Ina mika godiya ta musamman ga Alh. Armaya’u Sulaiman (Sarkin Daddawan Ablekuma Central), sannan shugaban matasan Bilbila. Ina mika godiya ta musamman ga sauran mukarraban fada bakidaya, ba zan iya cewa sai na kira sunan kowa da kowa ba, amma a gurguje akwai Haj. Fati Sarauniya (Sarauniyar Zangon Accra), akwai Haj. Hauwa (Majidadiyar Accra, akwai Haj. Magajiya (Magajiyar Zangon Accra), akwai Haj. Gado (Wakiliyar Bare-bari), akwai Hajiya magajiya (Wakiliyar Wangarawa), Akwai Uncle Sonihi (Sarkin Jaddada zaman lafiya na Wangarawa), Da Dan’masani (Wangarawa). Ina mika godiya ga dukkanin mukarraban wannan fada masu daraja, Alhamdulillah Ala kulli hal, ina yi wa kowa fatan alkhairi.
Me za ki ce ga masoyanki?
Ina son masoyana na fadin duniya su tayani addu’a da fatan alkhairi, da fatan Allah ya sa mu gama lafiya. Ina kira ga masoyana idan an ga zan yi abin da ba daidai ba a biyo ta social media a sanar da ni, domin in gyara. In an ga zan yi kuskure a bani shawara ta kafafen sadarwa, inda sako zai same ni cikin sauki. Makiya kuma ina so su kara sako ido saboda sai da gishirinsu muke samun suga, a fuskar makiyi muke gane aikin mu ya yi kyau ko bai ba. Allah ya karo mana dubun makiya dan mu ba ma so su yi kasa.
Wassalamu Alaikum.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wannan sarauta
এছাড়াও পড়ুন:
Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda yake ziyarar aiki a kasar Oman ya gana da manzon musamman na MDD a kasar Yemen Hans Grundberg a jiya Litinin ya yi tir da yadda Haramtacciyar Kasar Isra’ila take keta dokoki tana kai wa kasashen wannan yankin hare-hare.
Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Iran ya kuma nuna kin amincewar jamhuyriyar musulunci ta Iran da yadda ake ci gaba da killace kasar Yemen, yana mai yin gargadi akan sakamakon da zai biyo bayan keta doka da ‘yan Sahayoniya suke yi da shi ne ci gaba da hargitsi da fadace-fadace a wannan yankin.
A nashi gefen manzon musamman na MDD a kasar Yemen ya bukaci ganin Iran ta ci gaba da bai wa Majalisar Dinkin Duniyar hadin kai domin kyautata rayuwar al’ummar kasar ta Yemen da kuma shimfida zaman lafiya.
A wani labari mai alaka da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta amabci cewa za a yi ganawa a tsakanin minista Abbas Arakci da takwaransa na Faransa Jean Noel Baro a gobe Laraba 26/ Nuwamba a birnin Paris.
Jigon tattaunawar shi ne bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu da kuma batun furusunonin Faransa da suke a Iran.
Haka nan kuma tattaunawar bangarorin biyu za ta tabo halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya, sai kuma Shirin Iran na makamashin Nukiliya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci