Aminiya:
2025-10-13@14:51:01 GMT

Wata mata ta banka wa kanta wuta a Bauchi

Published: 4th, October 2025 GMT

Wata mata ta zuba wa kanta man fetur sannan ta banka wa kanta wuta a Jihar Bauchi.

Matar wadda mai matsakaicin shekaru ce, ta yi wannan aika-aika ne a ƙofar gidan tsohon Fira Ministan Najeriya, Marigayi Sa Abubakar Tafawa Ɓalewa.

Shaidu sun ce bayan saukar matar daga wani babur mai kafa uku, riƙe da galan ɗin man fetur a hannunta, ta nemi ganin Yelwa Abubakar, ’yar Marigayi Tafawa Ɓalewa, wadda ita ce Shugabar Hukumar Kula da Yara Masu Rauni da Marayu ta Jihar Bauchi (BASOVCA).

Amma da aka shaida mata cewa Hajiya Yelwa ba ta nan, sai matar ta zuba wa kanta fetur ɗin ta kuma kiyasta wa kanta ashana a babbar ƙofar shiga gidan.

Duk ƙoƙarin mutanen da ke wurin na kashe wutar ya gagara, sai daga baya aka garzaya da ita zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa (ATBUTH), inda daga bisani ta mutu a sakamakon munanan raunukan da ta samu daga ƙunar.

Shaidu sun bayyana cewa akwai alamar taɓin hankali a tare da matar.

Kakakin ’yan sandan jihar, Mohammed Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya mai bayyana takaici bisa haka.

Ya ce kwamishinan rundunar, Sani-Omolori Aliyu, ya ba da umarnin gudanar da bincike don gano ainihin abin da ya faru a ranar Juma’a 26 ga watan Satumba, 2026 ta gabata.

Ya bayyana cewa an yi nasarar yi wa matar tambayoyi a gadon asibiti, amma ta yi iƙirarin cewa ba ta san cewa fetur ne a cikin jarkar da ke hannunta ba, da kuma dage cewa ta ɗauka ruwa ne.

Wakil ya ce bayan zurfafa bincike an gano cewa matar tana da tarihin taɓin hankali, wanda maƙwabta suka ce matsalar ta ƙaru bayan ta  haifu autanta.

Ya ce tuna aka mika gawar ga iyalan mamaciyar domin yi mata jana’iza.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tafawa Ɓalewa

এছাড়াও পড়ুন:

An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

Sufeton ƴansanda na Ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya maye gurbin Kwamishinan ƴansandan birnin tarayya, CP Ajao Adewale, sakamakon ƙaruwar matsalolin tsaro a Abuja. Wannan mataki ya biyo bayan matsin lamba da yake fuskanta saboda rashin gamsuwa da aikinsa tun bayan karɓar ragama daga CP Benneth Igwe.

Majiyoyi daga cikin rundunar sun bayyana cewa sauya shi ya shafi yadda matsalolin tsaro ke ƙaruwa a Abuja, musamman bayan harin fashi da makami da ya yi sanadin mutuwar mai gabatar da shirye-shiryen gidan talabijin ɗin ARISE, Somtochukwu Maduagwu, da mai gadi Barnabas Danlami, a Katampe, ranar 29 ga Satumba, 2025.

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna  NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

Wata wasiƙar cikin gida daga shalƙwatar ƴansanda ta tabbatar da cewa CP Miller Gajere Dantawaye ne aka naɗa sabon kwamishinan ƴansanda na FCT, yayin da DCP Wilson Aniefiok Akpan aka tura shi zuwa jihar Kogi.

Wasiƙar, mai lamba TH.5361/FS/FHQ/ABJ/SUB.6/213, ta bayyana cewa wannan sauyin na ɗan lokaci ne har sai hukumar aiyukan ƴansanda ta ƙasa (PSC) ta amince da cikakken naɗin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar October 12, 2025 Manyan Labarai Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor October 12, 2025 Manyan Labarai Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna  October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya