Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Published: 4th, October 2025 GMT
Bincike ya kuma kai ga cafke wani bangare na kungiyar karkashin jagorancin Babangida, wadanda aka gano sun hada da Isah Musa da Usman Abdullahi, wadanda suka amsa laifin karya shaguna da kuma yin fashi a yankin Rigasa.
Lokacin bincike, wadanda ake zargin sun ambaci masu karbar kayan sata da suka taimaka musu wajen sayar da su.
Haka kuma, a ranar 10 ga Satumba, an kama wani mai suna Bello bisa zargin satar waya. Kamen nasa ya kai ga kwato wayoyi hannu 45 da kwamfutar tafi-da-gidanka, tare da kama masu karbar kayan sata nasa.
A wani nasara daban, a ranar 15 ga Satumba, tawagar sintiri daga sashen ‘yansanda na Kabala West ta tare wasu, Hassan (mai shekaru 19) da Abubakar (mai shekaru 21), a Unguwar Mu’azu Bypass. An kwato babur baki kirar TBS da bindigar 9mm pistol tare da harsasai uku daga hannunsu.
Haka kuma, a ranar 18 ga Satumba, jami’ai sun cafke Simon Haruna daga Karamar Hukumar Barikin Ladi, Jihar Filato, a Lambar Zango, Birnin Yaro, cikin Karamar Hukumar Igabi. Ana zargin yana tattaunawa kan sayar da bindigar Beretta pistol kafin a kama shi.
Tawagar ta kwato bindigar Beretta da aka kera a Amurka tare da harsasai uku daga hannunsa.
Kwamishinan ‘Yansanda, CP Rabiu Muhammad, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin bisa kwarewa, tare da tabbatar wa da mazauna jihar cewa rundunar ta himmatu wajen kawar da miyagun ‘yan ta’adda daga Jihar Kaduna.
Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da kasancewa cikin shiri da fadakarwa, tare da bayar da muhimman bayanai ga ‘yansanda a kokarin hadin gwiwa na tabbatar da tsaron jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Wayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
Ana zargin wata amarya da yi wa angonta yankan rago kwana uku bayan ɗaurin aurensu a Jihar Katsina.
Angon mai suna Abubakar Abdulkarim da aka fi sani da Dan Gaske, ana zargin ya rasa ransa bayan da amaryar ta yi amfani da wuƙa wajen halaka shi.
Shaidu sun ce ta yi masa mummunan rauni a wuya wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Angon da amaryarsa suka daura aure ne a ranar Alhamis, 18 ga Nuwamba, 2025, amma farin cikin aure ya rikide zuwa makoki a ranar Lahadi da rana lokacin da lamarin ya faru.
Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke FuskantaWani ɗan uwansa mai suna Aminu Danladi ya ce cewa sun yi taro da marigayin da safiyar ranar, suna shirya ziyarar ’yan uwansu da za a kai da yamma.
Ya ce daga baya ango ya koma gida domin shiri, sai kuma aka ji labarin an same shi kwance a cikin jini babu rai.
Aminu ya kuma ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa auren dole ne aka yi wa ma’auratan, inda ya tabbatar da cewa dangantakarsu ta kasance lafiya kafin aure.
Majiyoyi sun ce matar, ’yar asalin Katsina, ta taɓa yin aure a baya, abin da ake zargin dangin mijin ba su sani ba.
An ce bayan faruwar lamarin amaryar ta ruɗe inda ta je gidan maƙwabta tana neman abinci. Wannan hali ya sa tsofaffin mata zargin akwai matsala, suka bi ta gida inda suka tarar da gawar mijin, suka kuma sanar da jami’an tsaro.
Rundunar ’Yan Sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara gudanar da bincike a kai.
Kakakin ’yan sanda na jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargi da hannu a lamarin, kuma bincike na ci gaba.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Katsina, CP Bello Shehu, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike mai zurfi, tare da kira ga jama’a da su bayar da bayanai masu amfani.