HausaTv:
2025-11-27@20:27:37 GMT

Sheikh Qassem: Ba za mu mika makamin gwagwarmaya ba

Published: 28th, September 2025 GMT

Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qassem ya tabbatar da cewa gwagarmaya ba za ta  bari a kwance damarar ta ba, kuma za ta shiga fada irin na Karbala idan hakan ya kama, ya kara da cewa: “Za mu fuskanci duk wani aiki da zai yi wa Isra’ila hidima, ko da kuwa an mayar da shi tamkar wani aiki na kasa.

A jawabin da ya gabatar a yayin zagayowar cikar shekara guda da shahadar Sayyed Hassan Nasrallah da Hashem Safieddine, Sheikh Qassem ya mayar da martani ga kalaman manzon Amurka Tom Barrack, wanda ya ce Washington na son kwance damarar kungiyar Hizbullah, kuma ba za ta ba sojojin makamai domin tunkarar Isra’ila ba. Ya kara da cewa ” kwance damarar makamai na nufin kwance damarar dakarun gwagwarmaya bukata ce ta Isra’ila domin cimma manufofinta.

Sheikh Qassem ya yi kira ga gwamnatin Lebanon da ta cika aikinta na sake gina wuraren ‘ya kasar da Isra’ila ta rusa tare da ware kasafin kudi domin hakan, koda kuwa kadan ne. Ya nanata cewa Fifita maslahar kasa dole ne ya kasance kan gaba a cikin ajandar, kuma cimma hakan na bukatar hana Isra’ila ci gaba da zama a Lebanon.

Ya kara da cewa kiyaye hadin kai na cikin gida da kuma yin aiki don farfado da kasar Labanon ya zama wajibi,  kuma gwagwarmayar al’ummar kasar ita ce tushen karfinta.

Ya kuma yi kira da a aiwatar da yerjejeniyar Taif, wadda ta tanadi cimma nasarar ‘yantar da dukkanin yankunan kasar Lebanon da Isra’ila ta mamaye ta hanyar gwagwarmaya.

Ya ci gaba da cewa, “Muna goyon bayan gudanar da zaben ‘yan majalisar dokoki a kan lokaci,” yana mai cewa “gwamnati ta yi wani babban kure a lokacin da ta yanke shawara kan batutuwa da suka shafi makaman Hizbulah.”

Ya kara da cewa, suna son sojojin kasar Lebanon su yaki mutanensu, kuma muna goyon bayan sojoji  wajen tunkarar makiya na hakika, kuma a kodayaushe muna tare da su.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran: Kisan Nasrallah ya saba wa kundin tsarin mulkin MDD September 28, 2025 Shugaban Argentina ya nemi jinkirta ziyarar Netanyahu a kasar saboda fargabar boren jama’a September 28, 2025 Sojojin Isra’ila Sun Kashe Sama Da Falasdinawa 77 A Gaza A Yau Kawai. September 27, 2025 An Gudanar Da Taron Cika Shekara 1 Da Shahadar  Sayyid Nasrullah September 27, 2025 Yunkurin Jinkirta Dawo Da Takunkumi Kan Kasar Iran Bai Yi Nasara ba. September 27, 2025 Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce Shirin Nukiliyar Iran Na Zaman Lafiya Ne September 27, 2025 Shugaban Majalisar Tsaron Kasar Iran  Dr Ali Larijani  Ya Isa Birnin Berut . September 27, 2025 Iran ta kira jakadunta daga Birtaniya, Faransa, da Jamus domin tuntuba September 27, 2025 MDD : Isra’ila na kai harin bam a Gaza kowane minti 8 ko 9 September 27, 2025 MSF ta dakatar da ayyukan birnin Gaza saboda hare-haren Isra’ila September 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ya kara da cewa ya kara da cewa kwance damarar

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya kafa tarihin zama mutumin da ya fi kowa yawan zuri’ar da ta haddace Alkur’ani a tarihin duniya.

Alkaluma sun nuna cewa shehin malamin, wanda a kwanan nan ya cika shekara 100 a duniya, yana da ’ya’ya da jikoki da ma tattaba-kunne kusan 300 da suka haddace Alkur’ani.

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya

A cewar kundin tattara bayanai na Cholan Book Of World Records, wadanda suka karrama malamin da lambar yabo, Sheikh Dahiru Bauchi shi ne mutum na farko da ya taba samun irin wannan baiwar.

Bayanai sun nuna fitaccen malamin yana da ’ya’ya 95 da jikoki 406 da tattaba-kunne 100. Daga cikin wannan adadin, ’ya’yansa 77 da jikoki 199 da kuma tattaba-kunne 12 ne suka haddace Alkur’anin.

A ranar Alhamis, 27 ga watan Nuwamban 2025 ce Allah ya yi wa shehin malamin rasuwa a Bauchi.

Yana daga cikin Halifofin Sheikh Inyass

Sheikh Darihu Bauchi ne daga cikin halifofin Shehu Ibrahim Inyass, Halifan Darikar Tijjaniyya, bayan wanda ya assasa ta, wato Sheikh Ahmadu Tijjani.

Yana daga cikin manyan malaman Musulunci a Najeriya, shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Koli da ke bayar da Fatawar Musulunci a Najeriya sannan babban jigo ne a Darikar Tijjaniya a Najeriya da ma Afirka.

A zantawarsa da ’yan jarida shekarun baya a Bauchi, Sheikh Dahiru ya ba da takaitaccen tarihinsa, inda ya ce, “Tarihina dai ni Bafulatani ne, dukanin kakannina hudu Fulani ne, domin kowane mutum yana da kakanni hudu — ta wajen mahaifinsa biyu, ta wajen mahaifiyarsa biyu.

“To ni dukanin kakannina Fulani ne babu inda muka hadu da wata kabila ta kowace fuska. Mu Fulanin Bauchi ne a lokacin da Jihar Bauchi take hade da Jihar Gombe.

“Bayan da aka raba Jihar Bauchi da Jihar Gombe, sai muka zama mu Fulanin Jihar Bauchi ne, a lokaci guda kuma Fulanin Jihar Gombe ne.

“Ta wajen mahaifina ni Bafulatanin Jihar Bauchi ne, ta wajen mahaifiyata ni Bafulatanin Nafada ne da ke Jihar Gombe.

“An haife ni ne a watan Janairun 1927, wanda ya yi daidai da watan Muharram 1346 Bayan Hijira, a ranar Laraba.”

‘Yadda na mayar da karatun Alkur’ani sana’ata’

Ya ce abin da ya fi ba shi sha’awa a rayuwarsa shi ne irin yadda ya mayar da Alkur’ani sana’arsa da kuma yadda ya rungumi Darikar Tijjaniya ta zama rayuwarsa.

“A duk lokacin da nake hutu ina shagaltuwa ne da karatun Alkur’ani da karanta Salatul Fatihi da tasbihi da istigfari da salatin Annabi (SAW) da sauran zikirori,” in ji shi.

Kwarewar Sheikh Dahiru Bauchi

Da aka tambaye shi kan fannonin ilimin da ya fi kwarewa, shehin malamin ya ce, “Na yi dukkan karatuna na addini a karkashin kulawar mahaifina, har na haddace Alkur’ani kuma ta hannunsa ne na karbi Darikar Tijjaniya.

“Shi mahaifina ya karbi Darikar Tijjaniya ne ta hannun wani mutum mai suna Alhaji Gwani Abba, daga baya sai mahaifina ya ba ni izinin na tafi duk inda nake so domin zurfafa ilimina na addini da haddar Alkur’ani mai girma.

“Bangaren da na fi kwarewa sosai shi ne Alkur’ani, daga nan kuma sai bangaren Tafsiri, a nan malaman Tafsiri sun ce lallai na iya tafsiri inji su.

“Sai kuma bangaren Ma’arifa, ma’anar Ma’arifa shi ne ilimin (gyaran) zuciya wanda ake kiran sa Tlimin Tarbiyya.

“A nan ma masu irin ilimin kan ce ina da sani a fannin. Shehu Ibrahim ya ce lallai na san wannan bangare.

“Sauran ilimomi kuma ina tattabawa, su Hadisi da Lugga da Li’irabi da Tasrifi da Fikihu, duk ina tattabawa,” inji shi.

‘Dalilin da nake buga misali kan duk tambayar da aka yi min’

Da aka tambayarsa cewa jama’a na mamakin yadda idan aka yi masa tambaya sai ya ba da misali kafin ya bayar da gundarin amsar, sai ya ce, “Wato shi buga misali wata runduna ce ta Allah mai shigar da ilimi cikin kawunan mutane.

“Idan ka kawo amsar magana sai ka buga misalin da za ta hau kan mutane domin fahimtar da su.

“Shi buga misali yana jawo hankali a fahimci mene ne aka fada. Misali na da matukar muhimmaci wajen ba da amsa.”

Shehin malamin ya zama masanin Tafsirin Alkur’ani Mai Girma wanda ya samu lambobin yabo a wannan bangaren.

Ya kuma samu digirin girmamawa a bangarori daban-daban a Najeriya da ma kasashen waje.

Jami’ar Tarayya da ke Lafiya a Jihar Nasarawa ta ba shi lambar yabo ta Digirin girmamawa, sannan Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar girmamawa ta kasa ta OFR.

Nasarorin Sheikh Dahiru Bauchi

Ga wasu daga cikin nasarorin da Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya samu a tsawon shekarunsa:

Ya musuluntar da dubban mutane A duk lokaci bayan lokaci yakan karanta Alkur’ani kuma yana yin saukar Alkur’ani a kwana biyu Ya ba da lazumin Darikar Tijjaniyya wa dubban mutane da dama a fadin duniya Ya kafa makarantun haddar Alkur’ani sama da 1500 a Najeriya da sassan Afirka Sama da mutum 140,924 sun haddace Alkur’ani a makarantunsa a fadin Najeriya Karkashin gidauniyasa, an gina dakunan karatu guda 133,060 a Arewacin Najeriya Mutum ne mai kishin kasarsa Najeriya wanda aduk lokacin da ya bude baki zai yi addu’a sai ya roki Allah Ya ba kasar zaman lafiya da kwanciyar hankali

Bugu da kari, malamin yana cikin wadanda suka fi kowa dadewa suna tafisirin Alkur’ani da watan azumin Ramadan.

Masallacin da yake tafsirin da ke unguwar Tudun Wada a Kaduna, na daya daga cikin manyan masallatan da ke cikin garin, kuma za a iya cewa a tsawon shekaru, malamin yakan zauna a garin kusan fiye da a ko ina.

Wani bincike da wani wanda yayi Nazari kan rayuwar malamin ya kuma rubuta littafi a kansa mai suna Shehu Dahiru Bauchi Ginin Allah, shekaru uku da suka wuce, Farfesa Khalid Abdullahi Zaria, ya ce

Daya daga cikin almajiran shehin, Mallam Ahmad Tijjani Kolo, ya ce a yanzu an sami karin mahaddata a cikin zuri’arsa, inda yanzu suka doshi 300. Ya ce da wahala a sami mai irin wannan a tarihi.

Shugaban Kungiyar Daliban Sheikh Dahiru Bauchi, Mallam Ibrahim Imam Ismaila, ya ce a tarihi babu wanda ya taba samun irin baiwarsa.

‘Rayuwarsa gaba daya makaranta ce’

Shi kuwa Daraktan  Wakafi a Hukumar Shari’a na Jihar Bauchi, Mallam Ahmad Tijjani Sa’id, ya ce rayuwar shehun malamin gaba dayanta makaranta ce.

Ya kuma ce malamin ya yi tafiya daga Arewa har kasashen Kudu a kan jaki da doki don yada addinin.

Sannan ya yi tafiya a kan keke zuwa kauyuka da dama kamar Tafawa Balewa da yankunan Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Yamma don yada addinin Musulunci.

‘Gidajensa 1,000 da ake zama kyauta’

Malam Ahmad Tijjani Sa’id ya ci gaba da cewa babu abin mamaki cikin sha’anin malamin kamar yadda yake daukar nauyi ba tare da jin tsoron hidima ba.

“Yana da gidaje fiye da dubu daya a fadin kasar nan, amma ba inda ake haya, bayin Allah masu neman ilimi yake zubawa a ciki kyauta.

“Jama’ar da yake ciyarwa Allah kadai Ya san adadinsu. A kullum idan Shehi zai fito zai sallami baki fiye da 3,000 da suka zo ziyarar sa daga ciki da wajen Najeriya, kuma za ka samu dalibansa ya yi musu auren fari ya musu suna kuma bai gaji ba.

“Ya maka mace ta biyu ya dauki nauyinku. Ire-iren wadannan halaye na Shehi da wuya ka samu wanda zai iya yin haka.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin