Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

An haife ni a unguwar Tudun Nufawa dake Kano Municipal, na yi karatun firamare a jakara ‘Special Pramary School’, na yi sakandare a Gwammmaja 2. Sannan babban Sakandare a ‘GSS Dala’. Na yi karatun ‘Diploma’ a fannin ‘computer’, sannan na yi ‘National Diploma’ akan lafiyar hakori ‘Dental Surgery Technician’.

 

Ya batun iyali, shin akwai ko babu?

Ina da Aure, mata ta daya da ‘ya’ya biyar biyu maza uku mata.

 

Wane rawa ka ke takawa a cikin masana’antar Kannywood?

Na farko zan iya cewa ni ‘film maker’ ne, amma nafi karfi a ‘directing’. Sannan ina ‘Camera’ ina rubutu, Ina ‘acting’, Ina ‘Editing’.

 

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?

Tun daga kallon indiya ‘da’ da ake yi Asabar da Lahadi, sannan na kasance ina san kallon irin fina-finan ‘cartoon’ a lokacin muna makarantar sakandare a shekarun baya wajan 1996, mai suna Bakandamiyar Rikicin Duniya’. Ana yin wasu fim din hausa wadanda suka fara jan hankalina wajan tunanin ina da abin da zan iya a harkar fim. Akwai wani yayana wanda muke yin komai tare mai suna Hassan Mijinyawa, muka yi shawara akan yadda za mu kirkiri wani fim da za mu yi. Muna cikin shirye-shirye mu akwai wani daya daga cikin dan’uwan mu ya yi karatun da ya shafi fim, aikin jarida yana ba mu karfin gwiwa sai Allah ya karbe shi wato ya rasu a shekara 1998 mai suna Yusif Mijinyawa. Sai muka yi shiru zuwa wani lokaci, kafin 2000 muka dawo da karfin mu inda muka fara yin aikin fim ka’in da na’in.

 

Za ka yi kamar shekara nawa da fara harkar fim?

A kallla shekara ashirin da biyar.

 

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

Maganar kantawaye ni dai ban santa ba, dan ba a yi min ba.

 

Ya batun iyaye lokacin da za ka sanar musu kana sha’awar shiga harkar fim, ko akwai wani kalubale da ka fuskanta daga gare su?

Gaskiya ni dai ban samu wata matsala ba sai dai kawai nasihohi da kuma lallai mutun ya kula da kansa da addini sa kada kayi wani abu da zai keta ma mutumci sun bani goyan baya dari bisa dari.

 

Mu dan koma baya kadan, cikin abubuwan da ka lissafo wanda kake taka rawa cikin masana’antar, da wane bangare ka fara?

Daraktin, kuma har yanzu shi ne wanda na fi so.

 

Kafin ka fara daraktin, shin ka koya ne a wajen wani, ko kuwa ka shiga masana’antar ne da iyawarka?

E, gaskiya farkon shiga ta ganin yadda ake yi nayi na fara, amma daga baya na je sani online da ‘workshop’ da wasu karatuttuka da suka shafi harkar fim.

 

Ya farkon fara daraktin dinka ya kasance?

E, gaskiya ban sami wani kalubale ba, saboda wadanda na fara aiki da su sun bani hadin kai, sosai duk da cewa duk inda ka fara dole akwai ‘yan masaloli da na fuskanta wajan rashin sabo. Ace ni ne nake daraktin wasu manyan jarumai akwai abinda ya taimakamin a lokacin na dau kwararrun ma’aikata.

 

A wane fim ka fara daraktin, kuma ya karbuwar fim din ya kasance, ga masu kallo?

Akwai wani fim na kamfani na mai suna ALLURA shi ne na fara daraktin, kuma a lokacin ya samu karuwa domin muna siyar da ‘right’ na CD tun daga siyarwa masu buga wannan CD aka maida kudi aka ci riba, ya karbu sosai a wajan mutane.

 

Wane abu ne ya fi baka wahala a bangaren daraktin?

To abinda yake bani wahala ko kuma haushi shene jarumina yaki yin abinda aka sashi wannan yana sani inji aikin ya fita daga raina

Za mu cigaba mako me zuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kannywood fara daraktin masana antar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11

’Yan bindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 11 mazauna garin Isapa da ke kusa da Eruku a Ƙaramar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

Harin ya faru ne sa’o’i kadan bayan sakin wasu masu ibada da aka yi garkuwa da su suna tsaka da ibada a coci.

An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi

A cocin CAC da ke Ekuru, ana gudanar da bikin godiya domin murnar ’yantar da mambobi 18 da aka yi garkuwa da su kusan wata guda da ya gabata, sai ’yan bindiga suka kutsa suka yi garkuwa da mutum 38 bayan sun harbe uku har lahira.

Sabon harin, wanda ya faru da misalin ƙarfe 6:00 na yammacin Litinin, an ce ’yan bindiga kimanin 20 zuwa 30 ne suka kai shi.

Bayanai sun una cewa maharan su rika yin harbi ta ko’ina yayin da suke kutsa cikin garin, lamarin da ya sa mutane suka ranta a na kare.

Wata tsohuwa ta ji rauni sakamakon harbin kan mai uwa da wabi.

Wani jagoran al’umma da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da lamarin, inda ya ce: “Mutane 11 aka yi garkuwa da su, bakwai daga cikin su ’yan gida ɗaya. Waɗanda aka sace sun haɗa da mace mai juna biyu, masu shayarwa biyu da kuma kananan yara.”

Shaidar y ace sunaye mutanen sun hada da Talatu Kabiru, 20, Magaji, 6, Kande, 5, Hadiza, 10, Mariam, 6, Saima, 5, Habibat (mahaifiya), Fatima Yusufu (mahaifiya), Sarah Sunday, 22 (mai juna biyu), Lami Fidelis, 23 (uwa mai shayarwa) da kuma Haja Na Allah, ita ma uwa mai shayarwa.

Shaidun gani da ido sun ce ’yan bindigar sun bi wasu sassa na garin, inda suka bar alamun ramukan harsashin harbe-harbe a bangon gidaje da ƙofofi.

An gano harsashin bindiga AK-47 da aka harba daga wurare da dama bayan ’yan bindigar sun ja da baya tare da mutanen da suka yi garkuwa da su.

Lamarin ya haifar da tsananin tashin hankali a yankin da makotan garuruwa, yayin da jami’an tsaro da ’yan sa-kai ke ƙara ƙoƙari wajen gano maharan da ceto waɗanda aka sace.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kwara, Adekimi Ojo, ya tabbatar da lamarin ga yana mai cewa: “Eh, lamarin ya faru, amma ba zan iya cewa komai da yawa ba yanzu ba. Ina gab da shiga Isapa daga Ilorin. Zan ba da rahoto idan na isa.”

A yanzu haka dai Najeriya na fuskantar ɗaya daga cikin mafi munin matsalolin tsaro a tarihin ta. Hakan dai ya haifar da rufe makarantu da dama, musamman a Arewacin ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi