Aminiya:
2025-11-03@21:34:48 GMT

An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mulki na biyu a Tanzaniya

Published: 3rd, November 2025 GMT

An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mulki na biyu a matsayin shugabar Tanzaniya, duk da tarzomar da ta ɓarke bayan zaɓen da aka gudanar a makon jiya.

A wani ƙwarya-ƙwaryar biki da aka gudanar cikin matakan tsaro a Dodoma, babban birnin ƙasar, an rantsar da shugabar a wani wurin da ba a bai wa mutane da dama sun halarta ba.

An kashe ’yan bindiga 19 yayin wani hari a Kano Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump

Riƙe da Al-Qura’ni a hannu guda, Shugaba Hassan ta ce “na yi alƙawalin yi wa ’yan ƙasa aiki tuƙuru, zan yi biyayya ga dokoki na ƙasa da mutunta kundin tsarin mulki.”

Baƙin da aka gayyata ne kawai aka bai wa damar halartar rantsar da Shugaba Hassan a bikin da aka haska duk da katse intanet, yayin da ake ci gaba da zaman ɗar-ɗar a ƙasar kan sakamakon zaɓen.

An ayyana Hassan, wadda ta hau mulki a shekarar 2021 bayan rasuwar tsohon shugabanta, a matsayin wadda ta lashe zaɓen Larabar makon da ya gabata da kashi 97.66% na ƙuri’un da aka kaɗa.

Sai dai ’yan hamayya sun yi watsi da sakamakon kan zargin maguɗi, suna mai cewar an yi amfani da ƙarfin da ya wuce ƙima kan masu bore bayan ɓarkewar zanga-zangar adawa da sakamakon zaɓen.

Hassan, mai shekaru 65, ta tsaya takara ne kawai da ’yan takara daga ƙananan jam’iyyu bayan da aka hana manyan masu ƙalubalantarta daga manyan jam’iyyun adawa biyu shiga takarar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sake fuskantar wani mummunan sakamako inda ta koma matsayi na 20, wato ƙarshen teburin gasar Firimiyar Nijeriya ta NPFL.

Wannan koma baya na zuwa ne bayan ta sha kashi a hannun Enyimba United a wasan mako na 11, wanda aka buga a filin wasa na Enyimba International Stadium da ke birnin Aba a Jihar Abia.

An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mulki na biyu a Tanzaniya An kashe ’yan bindiga 19 yayin wani hari a Kano

Ɗan wasan Enyimba, Bassey John, ne ya fara zura ƙwallo a ragar Pillars a minti na 27, kafin Edidiong ya ƙara ta biyu mintuna kaɗan kafin a tafi hutun rabin lokaci, lamarin da ya nuna ƙarara cewa masu masaukin baƙi sun fi ƙarfin Pillars a wasan.

Sakamakon ya bai wa Enyimba damar hawa zuwa matsayi na 6 a teburin gasar da maki 16 daga wasanni 11, yayin da Sai Masu Gida suka sake komawa matsayi na 20, wato a ƙarshen teburin.

Wannan na nuni da cewa ƙungiyar ta Kano Pillars tana cikin tsaka mai wuya a wannan kakar wasan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinawa Biyu Sun Yi Shahada A Nablus Da Khalil
  • Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mullki na biyu a Tanzaniya
  • Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce