Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya
Published: 3rd, November 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sake fuskantar wani mummunan sakamako inda ta koma matsayi na 20, wato ƙarshen teburin gasar Firimiyar Nijeriya ta NPFL.
Wannan koma baya na zuwa ne bayan ta sha kashi a hannun Enyimba United a wasan mako na 11, wanda aka buga a filin wasa na Enyimba International Stadium da ke birnin Aba a Jihar Abia.
Ɗan wasan Enyimba, Bassey John, ne ya fara zura ƙwallo a ragar Pillars a minti na 27, kafin Edidiong ya ƙara ta biyu mintuna kaɗan kafin a tafi hutun rabin lokaci, lamarin da ya nuna ƙarara cewa masu masaukin baƙi sun fi ƙarfin Pillars a wasan.
Sakamakon ya bai wa Enyimba damar hawa zuwa matsayi na 6 a teburin gasar da maki 16 daga wasanni 11, yayin da Sai Masu Gida suka sake komawa matsayi na 20, wato a ƙarshen teburin.
Wannan na nuni da cewa ƙungiyar ta Kano Pillars tana cikin tsaka mai wuya a wannan kakar wasan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kano Pillars
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA