Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Ginin Babban Asibitin Anka Da Aka Inganta
Published: 18th, May 2025 GMT
Sauran sassan da aka gyara da kuma saka kayan aiki sun haɗa da sashen Kulawa da Mata (ANC), ɗakin tiyata, ɗakin X-ray, sabon ginin hukunta asibiti, masallaci, gidan Babban Daraktan Lafiya (gidaje mai ɗakuna 3), da kuma sashen kula da yara, da dai sauransu.
A yayin jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, an kammala gyaran gine-ginen tare da sanya dukkan kayan aikin kiwon lafiya cikin kwangilar cikin watanni 12.
Gwamnan ya ce, “A shekarar da ta gabata ne aka fara gyaran wannan asibitin, kuma wani kamfanin cikin gida ne aiwatar da kwangilar.
“Saba hannun jarin ya mayar da asibitin zuwa wurin kiwon lafiya na zamani tare da na’urori na zamani, wannan ba shakka zai inganta jinya ga ‘yan jihar a garin Anka da kewaye.
“Ga al’ummar Anka da kewaye, wannan aiki na ɗaya daga cikin alƙawuran da muka ɗauka na samar da ribar dimokuraɗiyya da inganta rayuwar ‘yan ƙasa.
“Za mu ci gaba da ba da fifiko kan al’amuran ci gaba, tare da tabbatar da cewa al’ummarmu sun samu ingantaccen lafiya kuma da araha, ilimi, noma, hanyoyi, da sauran muhimman ababen more rayuwa a faɗin jihar nan.
“Zuwa ga ma’aikata da mahukuntan babban asibitin Anka, ina kira gare ku da ku tabbatar da gudanar da wannan cibiya mai inganci da kulawa, ina kuma roƙon ku da ku jajirce wajen samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga jama’armu.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
Gwamnatin Jihar Kano, ta haramta kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta tana, wadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, yake ƙoƙarin kafawa.
Gwamnatin ta ce kafa hukumar ya saɓa da doka, kuma zai iya zama barazana ga zaman lafiya a jihar.
Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – BagoA cikin wata takarda da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a ranar 8 ga watan Disamba, 2025, gwamnatin ta ce ta gano an fara ɗaukar mutane aiki a hukumar ba tare da neman izini ba.
Gwamnatin ta ce hakan ya saɓa wa Dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.
Da yake zantawa da ’yan jarida, Kwamishinan YaɗaLabarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce Hukumar Hisbah ce kaɗai doka ta amince da ita wajen gudanar da ayyuka a jihar.
Ya ce kafa wata ƙungiya ko hukuma ta daban ba bisa ƙa’ida ba na iya kawo cikas ga zaman lafiya.
Umarnin ya bayyana cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon ɗaukar mutane aiki, tara su, horas da su ko tura su domin kafa wata hukumar Hisbah mai zaman kanta a jihar.
Gwamna Abba, ya kuma ayyana ayyukan hukumar a matsayin haramtattu, tare da gargaɗin cewa duk wanda ya yi amfani da kayan Hisbah, alamominta ko ikonta ba tare da izini ba zai fuskanci hukunci.
Gwamnan, ya umarci jami’an tsaro, ciki har da ’Yan Sanda, DSS, NSCDC, da sauran hukumomin tsaro, da su binciki waɗanda suka kafa sabuwar hukumar.
Gwamnatin ta kuma gargaɗi jama’a cewa duk wanda ya shiga, ya goyi baya ko ya haɗa kai da sabuwar hukumar, zai fuskanci hukunci.
An shawarci waɗanda aka ɗauka aiki su fice daga hukumar nan take tare da komawa ofishin Hisbah, ko Ƙaramar Hukuma.
Umarnin ya kuma tanadi hukunci ga waɗanda suka saɓa wa dokar, ciki har da gurfanar da su a gaban kotu bisa laifin gudanar da taro ba bisa ƙa’ida ba, kwaikwayon hukumomin gwamnati, da kafa rundunar tsaro ba tare da neman izini ba.
Wannan umarni ya fara aiki nan take, kuma za a yaɗa shi a kafofin watsa labarun Gwamnatin Jihar Kano.