Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Published: 18th, May 2025 GMT
Ya ce da Kwankwaso bai yi tunanin samar da jami’ar Wudil ba, da wannan alherin ba za a same shi ba, suna gode wa sauran wadanda suke ba da gudummawa wajen habakar wannan jami’ar.
Alhaji Abdukadir ya yi kira ga magoya baya da masu tasowa cewa idan suka sami dama su yi koyi da jagoran Kwankwasiyya, wanda ya kafa jami’o’i guda biyu a Jihar Kano bayan makarantu na gaba da sakandare guda 24 da ya samar da kuma tura dalibai talakawa karatu kasashen waje da mafi yawa sun gama suna amfanar da ci gaban al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
Majalisar Dattawan Nijeriya ta bayyana shirin kafa dokar da za ta mayar da rantsar da shugaban kasar a kwaryar majalisar, maimakon yadda ake yi a dandalin taro na Eagle da ke tsakiyar birnin Abuja.
DW ta ruwaito cewa ita dai Majalisar Dokokin Nijeriya ta 10 ta yi fice wajen dauko batutuwan da ke haifar da cece-kuce, kama daga yunkurin mayar da yin zabe ya zama dole da kuma hukunta duk wanda ya ci mutuncin taken Nijeriya sai kuma wannan batu na amfani da doka domin sauya tarihin da aka daura dambarsa tun a shekara ta 1999 da aka sake kafa dimokuradiyya a kasar.
Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APCTun daga wannan lokaci kawo yanzu ana rantasar da shugaban kasar ne a dandalin taro na kasa na Eagle da ke birnin Abuja, wurin da ke bayar da dama ga dubban ’yan Nijeriya su cire kwarkwatar idanuwansu yayin rantsar da shugaban da suka zaba.
A yanzu Majalisar Dattawan na son canza wannan al’ada, har ma da gwama batun da sanya shugaban Nijeriya ya rinka jawabi ga ‘yan majalsar a duk ranar dimukurdiyya 12 ga watan Yuni.
Tuni wannan mataki ya janyo mayar da martani a Nijeriyar, musamman wadanda da su aka yi gwagwarmayar yanke cibiyar sake kafa dimokuradiyya a kasar.
Domin sauya batu na tarihi ga muhimmin al’amari muhimmi ne a Nijeriyar, musamman danganta shi da ranar 12 ga watan Yuni da aka soke zaben da ake dangata shi da mafi sahihanci.
Sabo dai akan ce tirken wawa, domin shekaru 26 kenan da sake kafa dimokuradiyya da ake rantsar da sabon shugaban Nijeriya a dandalin Eagle din da ke tsakiyar birnin duk bayan shekaru hudu.
Majalisar Dokokin Nijeriyar dai kan gwada ta ga martanin ’yan kasar a kan wasu al’amura, inda daga baya ta kan janye batun wanda shi ne damar da dimukurdiyya ta bai wa ’yan kasa.