Ayatullah Khamenei : “Ba inda Rundunar Amurka ta taba shinfida zaman lafiya “
Published: 18th, May 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya caccaki kalaman shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan a ziyarar da ya kai a kasashen yankin Gulf na Farisa, yana mai cewa kalaman abin kunya ne a gare shi da dukkan Amurkawa, kuma bai cancanci amsa ba.
Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin kungiyar masu bayar da ilimi daga sassan kasar.
Ya kara da cewa wasu kalaman na Trump ba su ma isa a mayar da martani ba, yana mai kiransu da cewa abin kunya ne ga shi kansa shugaban Amurka da kuma wulakanci ga al’ummar Amurka.
‘’Ikirarinsa na cewa yana son samar da zaman lafiya da tsaro, zencen banza ne’’ inda ya kara da cewa Amurka na baiwa gwamnatin sahyoniya tan-tan na bama-bamai tana jefa su kan yara, asibitoci da gidajen jama’a a Gaza, Lebanon da kuma duk inda ta ga dama.
A yayin rangadin da ya ke a kasashen yankin Gulf, shugaban na Amurka ya yi jawabai da dama na sukar Iran.
A ziyarar da ya kai kasar Saudiyya, Donald Trump ya bayyana cewa “shugabannin Iran sun mayar da hankali wajen sace dukiyar al’ummarsu domin tallafawa ayyukan ta’addanci da zubar da jini a kasashen waje.”
Bayan hakan kuma, ya bayyana a Qatar cewa Amurka da Iran na daf da kulla yarjejeniyar nukiliya, kafin ya bukaci Iraniyawa da su “tashi” kan wannan batu “in ba haka ba wani mummunan abu zai faru.”, kallaman da jagoran juyin juya hali da shugaban kasar ta Iran sukayi fatali dasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha Da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga domin tattaunawa a Turkiyya
Rasha da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga dukkansu domin gudanar da tattaunawa ta kai tsaye tsakanin kasashen dake rikici da juna.
Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya aike da tawagar Ukraine zuwa birnin Istanbul na kasar Turkiyya domin ganawa da wakilan Rasha domin tattaunawa kan zaman lafiya, amma shi da kansa ba zai je can ba, kamar yadda wani babban jami’in Ukraine ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP.
Jami’in ya ce “Shugaban ya yanke shawarar cewa Ukraine za ta shiga tattaunawa da Rasha a Istanbul amma Volodymyr Zelensky ba zai je Istanbul ba saboda taron “ba a matakin shugabanni ba.
Ita ma fadar Kremlin ta sanar da jerin sunayen wakilan kasar don tattaunawa da Ukraine a Istanbul.
Amma ta ce Shugaban kasar ko kuma ministan harkokin waje ba zasu jagoranci tawagar ba.
Shugaban tawagar kasar Rasha Vladimir Medinsky ya bayyana cewa, babban aikin shawarwarin da za a yi tsakanin Rasha da Ukraine shi ne kawar da musabbabin rikicin da samar da zaman lafiya mai dorewa.
Ya jaddada cewa Rasha na kallon sabuwar tattaunawar a matsayin ci gaba da shirin zaman lafiya da aka yi a shekarar 2022.
Rasha ta abkawa Ukraine ne a ranar 24 ga Fabrairu na 2022, bayan amincewa da Moscow ta yi da ‘yancin kai na Jamhuriyar Donbass.
Matakin da Kasashen yammaci da kawayensu suka yi tir da shi, tare da laftawa Rasha jerin takunmumai.