HausaTv:
2025-06-14@02:29:40 GMT

Yemen ta sake harba makami mai linzami kan Isra’ila

Published: 18th, May 2025 GMT

Wani makami mai linzami da aka harba daga kasar Yeman ya fada a yankuna Falasdinawa da aka mamaye.

Yemen ta jima da take kai hare-hare kan Isra’ila a matsayin nuna goyan baya ga al’ummar Gaza dake fuskantar mamaya da ukuba da kisan kare dangi daga Isra’ila.

A cikin bayanin da ya yi bayan harin, babban jami’in gwagwarmayar Ansarullah ta kasar Yemen Nasr al-Din Amer, ya yi ishara da yadda gwamnatin Isra’ila ta yi watsi da kiran da kasashen Larabawa suka yi na neman zaman lafiya, ya kuma jaddada cewa hare-haren da ke faruwa a yankunan da aka mamaye, shi ne yare daya tilo da gwamnatin Isra’ila ke fahimta.

Hare-haren na Yemen sun yi matukar tasiri wajen durkusar da tattalin arzikin Isra’ila baya ga haifar da tsada sosai ga wasu kayayaki a Isra’ila, yayin da a daya bangaren kuma wasu hare-haren kan tsayar da al’amura a filin jirgin sama na Ben Gurion, mafi mahimmancin ga Isra’ila.

A martanin da ta mayar, Tel Aviv ta kara zafafa hare-haren wuce gona da iri kan kasar Yemen.

Sai dai kuma dakarun na Yemen din sun lashi takobin ci gaba da kai hare-hare ba tare da kakkautawa ba, muddin gwamnatin kasar ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na kisan kiyashi da kuma kara tsananta hare-haren da take kai wa a zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

Wani ganau mai suna Kespan Iliya wanda shi ma mazaunin unguwar ne ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan unguwar na cikin barci lokacin da ‘yan bindigar suka iso cikin shigar kwamandoji, inda suka rika harbe-harbe kan mazauna unguwar.

 

LEADERSHIP ta fahimci cewa, sama da gidaje 96 ne kuma aka kone a Gyenbwas, al’ummar gundumar Langai ta karamar hukumar Mangu a yayin harin.

 

Kokarin jin ta bakin jami’im yada labarai na rundunar ‘Operation Save Haven (OPSH)’, Manjo Samson Zhakom ya ci tura domin wayarsa a kashe take a lokacin rubuta wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Sake Tunzura Iran Shirin Makamashin Nukiliyarta Zai Fuskanci Martani
  • Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu