HausaTv:
2025-07-03@05:46:35 GMT

Yemen ta sake harba makami mai linzami kan Isra’ila

Published: 18th, May 2025 GMT

Wani makami mai linzami da aka harba daga kasar Yeman ya fada a yankuna Falasdinawa da aka mamaye.

Yemen ta jima da take kai hare-hare kan Isra’ila a matsayin nuna goyan baya ga al’ummar Gaza dake fuskantar mamaya da ukuba da kisan kare dangi daga Isra’ila.

A cikin bayanin da ya yi bayan harin, babban jami’in gwagwarmayar Ansarullah ta kasar Yemen Nasr al-Din Amer, ya yi ishara da yadda gwamnatin Isra’ila ta yi watsi da kiran da kasashen Larabawa suka yi na neman zaman lafiya, ya kuma jaddada cewa hare-haren da ke faruwa a yankunan da aka mamaye, shi ne yare daya tilo da gwamnatin Isra’ila ke fahimta.

Hare-haren na Yemen sun yi matukar tasiri wajen durkusar da tattalin arzikin Isra’ila baya ga haifar da tsada sosai ga wasu kayayaki a Isra’ila, yayin da a daya bangaren kuma wasu hare-haren kan tsayar da al’amura a filin jirgin sama na Ben Gurion, mafi mahimmancin ga Isra’ila.

A martanin da ta mayar, Tel Aviv ta kara zafafa hare-haren wuce gona da iri kan kasar Yemen.

Sai dai kuma dakarun na Yemen din sun lashi takobin ci gaba da kai hare-hare ba tare da kakkautawa ba, muddin gwamnatin kasar ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na kisan kiyashi da kuma kara tsananta hare-haren da take kai wa a zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU

Kungiyar Tarayyar Turai EU ta bukaci a sake komawa teburin tattauna shirin nukiliyar Iran cikin gaggawa, inda take neman hadin kai a tsakanin Tehran da kuma Hukumar Kula da Makamashi ta Duniya IAEA.

Babbar jami’ar diflomasiyyar EU Kaja Kallas ta shaida wa Ministan Harkokin Kasashen Ketare na Iran, Abbas Aragchi cewar Brussels a shirye take ta shige gaba don ganin an koma teburin tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran bayan hare-haren Amurka a tashoshin makamashinsu.

HOTUNA: An yi jana’izar Dantata a Madina Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza

Bayan wata doguwar tattaunawa ta wayar tarho da jami’ar ta yi da Mista Argchi, ta wallafa a shafinta na X cewar ya kamata a koma tattaunawa kan makamashin Iran cikin gaggawa, kuma akwai bukatar hadin kai daga hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa domin cimma yarjejeniya.

Kazalika Kallas ta gargadi Tehran cewar duk wani yunkuri na janyewa daga tattaunawar ka iya dagula al’amura.

Wannan na zuwa ne bayan da Tehran ta yi watsi da sake komawa kan teburin tattaunawa da hukumar ta yi, inda Tehran ta ce tana bukatar tabbacin Amurka ba za ta sake kai mata hari ba.

A baya dai EU ta kasance mai shiga tsakani a yarjejeniyar nukiliyar Iran na 2015 da aka cimma da manyan kasashen duniya, kafin daga bisani Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi watsi da yarjejeniya a shekarar 2018.

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
  • Iraki Ta Kai Karar HKI Kan Amfani Da Sararin Samaniyar Kasar Don Kaiwa Iran Hare hare
  • Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Iran Tana Tababa da Ayyukan Hukumar Makamashin Nukl’ila Ta MDD Wato IAEA A  Halin Yanzu
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa