Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon taya murna ga shugaban Iraqi Abdul Latif Rashid, wanda kuma shi ne shugaban karba-karba na majalisar shugabannin kasashen kungiyar Larabawa, tare da taya murnar kaddamar da babban taron kungiyar na 34, a birnin Baghdad na Iraqi.

Xi Jinping ya bayyana cewa, cikin shekaru sama da 80 da kafata, kungiyar kasashen Larabawa ta kasance mai mayar da hankali kan inganta hadin kai da karfafa yankin Larabawa da furta matsalolin kasashen da inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ya kara da cewa, a shirye kasar Sin take ta hada hannu da kasashen Larabawa wajen zurfafa aminci da ingiza hadin gwiwar moriyar juna da kara musayar al’adu da musaya tsakanin jama’a da hada hannu a tafarkin da kowannensu ya dauka na zamanantar da kansa da gina al’ummar Sin da ta Larabawa mai makoma ta bai daya. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar

Bayan hare-haren da kungiyoyin yan ta’adda masu iko da kasar Siriya suka kai kan wani Cuci a kasar Siriya jami’an gwamnatin kasar Siriya sun nuna damuwarsu da yiyuwar wadannan kungiyoyi su kawo hare-hare a cikin kasar ta Lebanon musamman a cikin wadan nan kwanaki na makokin Imam Hussain (a).

Wani Jami’in gwamnati a kasar ta Lebanon ya fadawa Jaridar da The National ta kasar Amurka kan cewa a makon da ya gabata an kama wani shugaban yan kungiyar yan ta’adda ta ISIS a cikin kasar, tare da zarginsa da shiri hare-hare masu yawa a kasar Lebanon.

Kafin haka dai a cikin watan da ya gabata wani dan ta’ada ya tarwatsa kansa a cikin wani coci a birnin Damascus babban birnin kasar Siriya inda ya kashe mutane 25.

Kungiyar yan ta’adda ta Daesh dai sun fara aiki karkashin kasa tun bayan da dakarun kungiyar Hizbulla.. da kuma sojojin kasar Lebanon sun fatattakesu a shekara 2017. Sannan a wasu lokutan sun kai hare-hare kan kungiyar Hizbullah a kasar.

Sannan bayan kungiyar HTS ta kwace mulki a hannun shugaba Asad a shekarar da ta gabata, har yanzun akwai yiyuwar barazanar hare-haren ISIS tana nan a kan kasar ta Lebanon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  • Kasashen Dimokaradiyyar Congo Da Ruwanda Sun Rattaba Hannu Kan Yrajejeniyar Zaman Lafiya