Leadership News Hausa:
2025-07-02@14:36:16 GMT

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Published: 17th, May 2025 GMT

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Kwanan nan ne Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da rahoton dake sabunta hasashen yanayin tattalin arzikin duniya gami da makomarsa na shekara ta 2025 a tsakiyar shekarar da muke ciki, inda rahoton ke ganin kara harajin kwastam da rashin sanin tabbas game da manufofin cinikayya sun janyo tabarbarewar makomar tattalin arzikin duk duniya, tare da haifar da tarin kalubaloli ga kasa da kasa, musamman kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin.

Rahoton na hasashen cewa, saurin karuwar tattalin arzikin duniya na bana, zai ragu zuwa kaso 2.4 bisa dari, yayin da saurin karuwar cinikayya zai ragu zuwa kaso 1.6 bisa dari. Kana, rahoton na ganin cewa, daidaita manufofi gami da hadin-gwiwar kasa da kasa, na da muhimmanci gaya ga samar da ci gaba ga tattalin arzikin duniya, da tabbatar da dorewarsa.

Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, abubuwa na zahiri sun shaida cewa, dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya muhimmin abu ne da kowa zai amince da shi, kuma bude kofa ga kowa da inganta hadin-gwiwa muhimmin abu ne da ya kamata mu yi a wannan zamanin da muke ciki, kazalika, ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban shi ne zabin da ya zama dole.

Kakakin ya kuma jaddada cewa, har kullum kasar Sin na tsayawa ga fadada bude kofarta ga kasashen waje, kuma bude kofar kasar Sin, dama ce ga duk duniya har abada. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tana Tababa da Ayyukan Hukumar Makamashin Nukl’ila Ta MDD Wato IAEA A  Halin Yanzu

Gwamnatin kasar Iran ta gargadi kasashen yammacin Asiya kan cewa mai yuwa yaki ya sake barkewa tsakaninta da HKI, akwai tababa kan cewa HKI zata kiyaye budewa juna wuta da ta cimma da kasar Iran.

Shafin yanar gizo na labarai ArabNews na kasar Saudiya ya nakalto Manjo Janar Abdulrahman Musawi babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran  yana fadar haka a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da ministan tsaro na kasar Saudiya Yerima Khalid bin Salman, ya kuma kara da cewa HKI ba kasashe abin amincewa ba. Musawi ya ce sojojin JMI a shirye suka su dakile dukkan hare-haren da HKI zata kawo nan gaba.

A wani bangare kuma shugaban hukumar makamashin nukliya ta kasa da kasa ta kuma MDD IAEA yace Iran tana iya sake fara aikin tace makamashin Uranium a cikin watanni masu zuwa . Rafael Grossi ya bayyanawa tashar talabijin ta CBS a ranar Lahadi kan cewa , bayana hare-haren Amurka kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran ba zamu iya cewa kome yak are kuma. Saboda ba wanda ya isa y araba kasar Iran daga fasahar nukliyar da take da shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
  • Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
  • Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci
  • Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
  • Iran Tana Tababa da Ayyukan Hukumar Makamashin Nukl’ila Ta MDD Wato IAEA A  Halin Yanzu
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  • Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Suna Shakku Kan Tsagaita Bude Wuta Zai Dore Da Isra’ila
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya