Leadership News Hausa:
2025-05-17@23:35:20 GMT

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Published: 17th, May 2025 GMT

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Kwanan nan ne Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da rahoton dake sabunta hasashen yanayin tattalin arzikin duniya gami da makomarsa na shekara ta 2025 a tsakiyar shekarar da muke ciki, inda rahoton ke ganin kara harajin kwastam da rashin sanin tabbas game da manufofin cinikayya sun janyo tabarbarewar makomar tattalin arzikin duk duniya, tare da haifar da tarin kalubaloli ga kasa da kasa, musamman kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin.

Rahoton na hasashen cewa, saurin karuwar tattalin arzikin duniya na bana, zai ragu zuwa kaso 2.4 bisa dari, yayin da saurin karuwar cinikayya zai ragu zuwa kaso 1.6 bisa dari. Kana, rahoton na ganin cewa, daidaita manufofi gami da hadin-gwiwar kasa da kasa, na da muhimmanci gaya ga samar da ci gaba ga tattalin arzikin duniya, da tabbatar da dorewarsa.

Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, abubuwa na zahiri sun shaida cewa, dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya muhimmin abu ne da kowa zai amince da shi, kuma bude kofa ga kowa da inganta hadin-gwiwa muhimmin abu ne da ya kamata mu yi a wannan zamanin da muke ciki, kazalika, ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban shi ne zabin da ya zama dole.

Kakakin ya kuma jaddada cewa, har kullum kasar Sin na tsayawa ga fadada bude kofarta ga kasashen waje, kuma bude kofar kasar Sin, dama ce ga duk duniya har abada. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Ce Ba Ta Tsoron Duk Wata Barazana Don Neman Tauyaye Mata Hakki

Shugaban kasar Iran ya jaddadacewa: Sun yi Imani da tattaunawa, amma ba su jin tsoron duk wata barazana

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa: Tabbas Iran tana gudanar da zaman tattaunawa da Amurka amma ba ta tsoron duk wata barazanarta, yana mai nuni da kalaman Trump da ke cin karo da juna, wani lokaci yana magana kan zaman lafiya sannan a wasu lokutan yana barazana da yaki.

A jawabin da ya gabatar a wajen bikin cika shekaru biyu da samun nasarar tawagar “Rukunin Jirgin Ruwa na 86” na sojojin ruwan Iran, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yaba da sadaukarwar da jaruman da suka yi wannan hidimar, yana mai cewa: “Suna alfahari da kasancewar dakarunsu, yana mai jaddada cewa; Ya ku masoya, hangen nesa na sojojin ruwa da dukkanin masu kare wannan kasa mai tsarki suke dauke da shi abin alfahari ne a gare kasar Iran.”

Ya kara da cewa: A kodayaushe ya yi imanin cewa: Iran ba za ta amince da kasance kasa da sauran kasashe a kowane fanni ba. Nasarorin da Iran ta samu wajen samar da jiragen ruwa na karkashin ruwa, masu dauke manyan makamai masu tarwatsa jirgi, da makamai da aka kera a cikin gida, ba tare da dogaro da bangarorin ketare ba, da mayar da Iran ta zama mai fitar da kayan soja zuwa kasashen waje, abin alfahari ne.

Shugaban ya yi gargadi kan yunkurin makiya na yada dabi’ar nuna gajiyawa a tsakanin al’ummar Iran, da haifar da sabani a tsakanin jami’ai, yana mai cewa: A karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci, hadin kai ya fi karfi a yau fiye da kowane lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Ce Ba Ta Tsoron Duk Wata Barazana Don Neman Tauyaye Mata Hakki
  • Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari
  • Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya
  • Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
  • Saudiya Ta Samar Da Wata Manhaja Ta Kiwon Lafiyar Mahajjata A Cikin Harsun 8 A Duniya
  • Jagora: Yin Shirun da  Kasashen Duniya Sun Yi Kan ABinda Yake Faruwa A Gaza Abun Mamaki Ne
  • Iran Da Kasashen Turai uku wato E3 Zasu Bude Tattaunawa A Tsakaninsu A Birnin Istambul A Gobe Jumma’a
  • ’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa