Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada
Published: 17th, May 2025 GMT
Kwanan nan ne Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da rahoton dake sabunta hasashen yanayin tattalin arzikin duniya gami da makomarsa na shekara ta 2025 a tsakiyar shekarar da muke ciki, inda rahoton ke ganin kara harajin kwastam da rashin sanin tabbas game da manufofin cinikayya sun janyo tabarbarewar makomar tattalin arzikin duk duniya, tare da haifar da tarin kalubaloli ga kasa da kasa, musamman kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin.
Rahoton na hasashen cewa, saurin karuwar tattalin arzikin duniya na bana, zai ragu zuwa kaso 2.4 bisa dari, yayin da saurin karuwar cinikayya zai ragu zuwa kaso 1.6 bisa dari. Kana, rahoton na ganin cewa, daidaita manufofi gami da hadin-gwiwar kasa da kasa, na da muhimmanci gaya ga samar da ci gaba ga tattalin arzikin duniya, da tabbatar da dorewarsa.
Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, abubuwa na zahiri sun shaida cewa, dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya muhimmin abu ne da kowa zai amince da shi, kuma bude kofa ga kowa da inganta hadin-gwiwa muhimmin abu ne da ya kamata mu yi a wannan zamanin da muke ciki, kazalika, ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban shi ne zabin da ya zama dole.
Kakakin ya kuma jaddada cewa, har kullum kasar Sin na tsayawa ga fadada bude kofarta ga kasashen waje, kuma bude kofar kasar Sin, dama ce ga duk duniya har abada. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arzikin duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Harkokin Shari’ar Kasa Da Kasa Na Iran Ya Yi Tofin Allah Tsine Kan Furucin Jami’ar Shari’ar Kasa Da Kasa
Mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da kasa da kasa ya mayar da martani ga son zuciya da wani jami’in kasa da kasa ke yi game da mamayar ‘yan sahayoniyya
Mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya yi tsokaci game da kalaman mataimakiyar shugaban kotun kasa da kasa (ICJ) na goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila, yana mai cewa: “Wannan wani lamari ne mai ban mamaki da ya saba wa ka’idojin shari’a da kuma ka’idar rashin son kai na shari’a.”
A wata sanarwa dayta fitar a dandalin X, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin shari’a da harkokin kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya rubuta cewa: “Wannan wani lamari ne mai ban mamaki da ya saba wa ka’idojin shari’a. Mataimakiyar shugabar kotun kasa da kasa ta fito fili ta bayyana goyon bayanta ga hukumar Isra’ila, yar mamaya da ake ci gaba da gudanar da shari’a da dama a gaban kotu.”
Gharibabadi ya kara da cewa: Wannan ra’ayi na nuna son kai yana zubar da mutuncin kotun kasa da kasa da kuma saba ka’idar amincin shari’a da rashin son kai.
Ya kamata a lura cewa mataimakiyar shugabar kotun kasa da kasa (ICJ) ta Uganda Julia Sebutinde, ta bayyana cewa “Allah yana goyon bayanta, kan tsayawa tare da Isra’ila,” bisa la’akari da cewa “wannan alamun ƙarshen duniya ne da ya bayyana a Gabas ta Tsakiya.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araqchi Ya Gode Wa Gwamnatin Iraki Da Al’ummarta Kan Kyakkyawar Tarbar Masu Ziyarar Arba’een August 16, 2025 Kungiyar Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Sanya Ta Cikin Jerin Sunayen Bakin Littafin Majalisar Dinkin Duniya August 16, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Tafka Muggan Ayyukansu A Yankin Zirin Gaza August 16, 2025 Mataimakiyar Shugaban Kotun ICJ Ta Ce Tana Goyon Bayan HKI August 16, 2025 Burtaniya Zata Gurfanar Da mutane 60 Saboda Goyon Bayan Falasdinawa August 16, 2025 Qalibof: Dole Ne Musulmi Su Hada kai Don Matsin Lamba Ga HKI August 16, 2025 Aragchi: Yiyuwan Sake Shiga Yaki Da HKI Nan Kusa Yana Da Wuya August 16, 2025 Putin da Trump sun bayyana aniyarsu ta kawo karshen rashin jituwa da warware batun Ukraine August 16, 2025 Takht-Ravanchi: Iran a shirye take ta ci gaba da tattaunawa kan hakkinta na nukiliya August 16, 2025 Sudan: Al-Burhan ya ce babu sulhu tsakaninsu da dakarun RSF August 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci