Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya yi watsi da wasu kalaman shugaban kasar Amurka Donal Trump a ziyar da ya kammala a wasu kasashen larabawa na yankin Tekun farisa, ya kuma bayyana wasu kalamansa a matsayin kungiya ga kansa da kuma mutanen Amurka. Har’ila yau Jagoran ya kara da cewa da dama daga cikin maganganunsa basu cancanci maida martani ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a yau Asabar, a lokacinda yake ganawa da wasu malaman makaransu daga larduna daban daban na kasar, a Husainiyyar Imam Khonaini (q) a nan Tehran.

Jagoran ya kara da cewa : Trump yace yana son amfani da karfin da Amurka take da shi don samar da zaman lafiya wanda karaye ce, saboda. Shi da jami’an gwamnatin Amurka da suna amfani da karfi wajen kashe mutanen Gaza, sannan suna farwa kasashe da yaki, inda zasu iya. Haka ma suna amfani da karfi wajen goyon bayan ma’aikatansu a kasashen duniya da dama don kare bukatu da manufofinsu a wadannan kasashe.

A wani wuri a jawabinsa jagoran ya bayyana cewa, gaskiya ne ana amfani da karfi don samar da zaman lafiya a wani lokaci, kamar yadda JMI take bunkasa karfinta na makamai da kuma dabarbarun yaki a ko wani lokaci.

Amma Amurka da kawayenta da dama suna amfani da karfinsu suna goyon bayan HKI don ta kashe yara a Gaza, ta rusa asbitoci a gaza, ta kuma rusa gidajen mutane a Gaza da Lebanon da Yemen da duk inda zasu iya yin haka.

Imam Khaminae ya sifanta HKI a matsayin mabubbukan barna da rashin zaman lafiya da cusa  gaba cikin kasashen yammacin Asiya. Yace ” HKI a wannan yankin tana kamar cutar daje ce, wacce dole a tumbuketa daga wannan yankin.

Dangane da fadin shugaba Trump kan cewa gwamnatocin kasashen yankin ba zasu iya tabbata a kan kujerun shugabancin kasashensu na kwana goma ba. Jagoran yace wannan ma kariya ce ba haka ba, wannan tsarin ya fada, tare da gwagwarmayan kasashen wannan yankin sai an kori Amurka daga cikinsa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci

Jagoran juyin musulunci na Iran wanda shi ne babban kwamandan rundunonin sojan kasar Iran, ya nada sabbin kwamandoji da maye gurbinsu da wadanda su ka yi shahada.

Bayan shahadar kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci Shahid Hussain Salami, da kuma  babban hshahid Muhammad Hussain Bakiri, sai Shahid Gulam Ali Rashid wanda shi ne kwamandan Bakirin soja na “Khatamul-Anbiya, jagoran juyin ya sanar da sunayen wadanda su ka maye gurbinsu.

Birgediya Muhammad Pakphur shi ne wanda jagoran ya sanar a matsayin sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci, sai kuma  Manjo Janar Musawi a mastayin sabon kwamandan rundunar sojan kasar, yayin da aka nada janar Ali Shadmani a matsayin kwamandan Barikin soja na Khatamul-Anbiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika