Jagora: Jawaban Trump A Ziyar Da Ya Kai Wasu Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Abin Kunya Ne Gare Shi Ga Kuma Amurkawa
Published: 17th, May 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya yi watsi da wasu kalaman shugaban kasar Amurka Donal Trump a ziyar da ya kammala a wasu kasashen larabawa na yankin Tekun farisa, ya kuma bayyana wasu kalamansa a matsayin kungiya ga kansa da kuma mutanen Amurka. Har’ila yau Jagoran ya kara da cewa da dama daga cikin maganganunsa basu cancanci maida martani ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a yau Asabar, a lokacinda yake ganawa da wasu malaman makaransu daga larduna daban daban na kasar, a Husainiyyar Imam Khonaini (q) a nan Tehran.
Jagoran ya kara da cewa : Trump yace yana son amfani da karfin da Amurka take da shi don samar da zaman lafiya wanda karaye ce, saboda. Shi da jami’an gwamnatin Amurka da suna amfani da karfi wajen kashe mutanen Gaza, sannan suna farwa kasashe da yaki, inda zasu iya. Haka ma suna amfani da karfi wajen goyon bayan ma’aikatansu a kasashen duniya da dama don kare bukatu da manufofinsu a wadannan kasashe.
A wani wuri a jawabinsa jagoran ya bayyana cewa, gaskiya ne ana amfani da karfi don samar da zaman lafiya a wani lokaci, kamar yadda JMI take bunkasa karfinta na makamai da kuma dabarbarun yaki a ko wani lokaci.
Amma Amurka da kawayenta da dama suna amfani da karfinsu suna goyon bayan HKI don ta kashe yara a Gaza, ta rusa asbitoci a gaza, ta kuma rusa gidajen mutane a Gaza da Lebanon da Yemen da duk inda zasu iya yin haka.
Imam Khaminae ya sifanta HKI a matsayin mabubbukan barna da rashin zaman lafiya da cusa gaba cikin kasashen yammacin Asiya. Yace ” HKI a wannan yankin tana kamar cutar daje ce, wacce dole a tumbuketa daga wannan yankin.
Dangane da fadin shugaba Trump kan cewa gwamnatocin kasashen yankin ba zasu iya tabbata a kan kujerun shugabancin kasashensu na kwana goma ba. Jagoran yace wannan ma kariya ce ba haka ba, wannan tsarin ya fada, tare da gwagwarmayan kasashen wannan yankin sai an kori Amurka daga cikinsa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi sauye-sauyen jagoranci a Hukumar Talabijin ta ƙasa (NTA), inda ya naɗa Rotimi Richard Pedro a matsayin sabon Darakta-Janar. Sauran naɗe-naɗen sun haɗa da Karimah Bello a matsayin Babbar Darakta ta Sashen Tallace-Tallace, Stella Din a matsayin Babbar Darakta ta Sashen Labarai, da Sophia Essahmed a matsayin Manajing Darakta ta Kamfanin NTA Enterprises Limited.
Pedro, ɗan asalin jihar Lagos, ƙwararren mai ba da shawara ne a harkar kafofin watsa labarai, mai gogewa sama da shekaru 30 a fannoni da suka haɗa da talabijin, haƙƙoƙin watsa wasanni, da dabarun tallace-tallace a Afrika, da Birtaniya da Gabas ta Tsakiya. Kwararre ne a fannin nishaɗi da mallakar fasaha, tare da digirin na biyu a Gudanar da Zuba Jari daga jami’ar City Business School, London.
2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – SoludoA 1995, ya kafa Optima Sports Management International (OSMI), wanda ya shahara wajen yaɗa manyan gasanni kamar Premier League na Ingila, da UEFA Champions League, da Gasar Cin Kofin Duniya ta FIFA, da wasannin CAF zuwa ƙasashe sama da 40. Haka kuma, ya yi aiki a manyan muƙamai a Bloomberg Television Africa, Rapid Blue Format, da kuma matsayin mai ba da shawara ga FIFA, da UEFA, da Fremantle Media, da Ƙungiyar Masu Watsa Labarai ta Afrika (AUB).
Masana sun bayyana Pedro a matsayin wanda ya yi fice wajen samar da kafafen yaɗa labarai masu ƙarfi a kasuwanci, da ƙara samun kuɗin tallafi, da kawo shirye-shirye masu inganci ga masu kallo a Afrika. Wannan naɗin na nuna manufar Gwamnatin Tarayya na sabuntawa da sake gina NTA domin ta yi gogayya a kasuwar watsa labarai ta zamani.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp