Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa  aiwatar da yarjeniyar zaman zaman lafiya wadanda aka cimma tsakanin kasashen Armenia da kuma Azerbaijan da gaggawa zai tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin kasashen biyu.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto Aragchi yana fadar haka a lokacin ganawarsa da sakataren majalisar koli ta tsaron kasar  Armenia, Armen Grigoryan  wanda yake ziyarar aiki a nan Tehran a yau Asabar.

Ministan ya kara da cewa JMI zata tabbatar da cewa an aiwatar da sulhu tsakanin kasashen biyu da gaggawa saboda tana dasawa da kasashen biyu makobta gareta.

A cikin watan Maris da ya gabata ne kasashen Armenia da Arzerbaijan suka amince a rubuta yarjeniyar sulhu a tsakaninsu a tsakaninsu don kawo karshen rikici a tsakaninsu wanda ya kusan shekaru 40 suna fafatawa a tsakaninsu.

Kasashen biyu sun yi yaki na karshe a tsakaninsu kan mallakar yankin Karabakh a shekara ta 2020 haka ma sun tabka yake-yake a kan malakar yankin a shekaru 1990 da bayansa, har zuwa lokacinda Azerbaijan ta kwace yankin a cikin sa,o,ii a yankin 2020. Sannan Armenia ta sallama mata yankin. Kasashen duniya dai sun amince da cewa yankin na Azerbaijan ne.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

Wani rikicin gado a kan fili da ya ɓarke tsakanin wasu ahali biyu a ƙauyen Kopkopshe na gundumar Tunkus da ke Ƙaramar Hukumar Mikang ta Jihar Filato, ya yi sanadiyyar mutuwar mutum ɗaya tare da ƙone gidaje da dama.

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, bayan aukuwar rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu wanda sun shafe fiye da shekaru biyu ba sa ga maciji a kan asalin mai haƙƙin gadon gonar daga iyayensu.

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Hadimin Shugaban Ƙaramar Hukumar Mikang kan harkokin yaɗa labarai, Nkat Joseph Lakai, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce shugaban ya ziyarci al’ummar kan abin ya faru tare da yin Allah-wadai wanda misalta da abin kunya.

A cewarsa hakan cikas ne ga ƙoƙarin gwamnati kan faɗi tashin da take na kare rayuka da dukiyar al’umma daga hare-haren ‘yan ta’adda da ma daƙile aikata munanan laifuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 
  • Sabani Tsakanin Bin Gafir, Smotresh Da Zamir Kan Makomar Fursinonin Yahudawa A Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA
  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda