Iran: Aiwatarda Yarjeniyar Zaman Lafiya Tsakanin Armenia Da Arzerbaijan Zai Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Kasashen Biyu
Published: 17th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa aiwatar da yarjeniyar zaman zaman lafiya wadanda aka cimma tsakanin kasashen Armenia da kuma Azerbaijan da gaggawa zai tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a tsakanin kasashen biyu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto Aragchi yana fadar haka a lokacin ganawarsa da sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Armenia, Armen Grigoryan wanda yake ziyarar aiki a nan Tehran a yau Asabar.
Ministan ya kara da cewa JMI zata tabbatar da cewa an aiwatar da sulhu tsakanin kasashen biyu da gaggawa saboda tana dasawa da kasashen biyu makobta gareta.
A cikin watan Maris da ya gabata ne kasashen Armenia da Arzerbaijan suka amince a rubuta yarjeniyar sulhu a tsakaninsu a tsakaninsu don kawo karshen rikici a tsakaninsu wanda ya kusan shekaru 40 suna fafatawa a tsakaninsu.
Kasashen biyu sun yi yaki na karshe a tsakaninsu kan mallakar yankin Karabakh a shekara ta 2020 haka ma sun tabka yake-yake a kan malakar yankin a shekaru 1990 da bayansa, har zuwa lokacinda Azerbaijan ta kwace yankin a cikin sa,o,ii a yankin 2020. Sannan Armenia ta sallama mata yankin. Kasashen duniya dai sun amince da cewa yankin na Azerbaijan ne.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Tabbas fannonin zamanintar da kai na Sin na iya zama babbar taswira da kasashen Afirka ka iya bi, wajen kaiwa ga bunkasa yankuna, da kyautata zamantakewar al’ummunsu, da samar da isassun damammaki na gudanar da kyakkyawar rayuwa mai cike da walwala ga al’ummun nahiyar.(Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp