Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
Published: 17th, May 2025 GMT
A makon da ya gabata, wasu ma’aikatan hukumar ilimi ta ƙaramar hukumar Damboa guda biyu sun mutu a irin wannan hari a hanyar Damboa zuwa Maiduguri.
’Yan ta’addan Boko Haram sun dawo da amfani da bama-bamai da suke birnewa a hanya domin kai hari kan matafiya da motocin da ke amfani da manyan hanyoyin Jihar Borno, abin da ya janyo asarar rayuka da dama a baya-bayan nan.
A halin yanzu kuma, dakarun sojin Nijeriya na ci gaba da kai farmaki a dazukan Sambisa da sauran maɓoyar ’yan ta’adda a faɗin jihar domin murƙushe su da kawar da su gaba ɗaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Boko Haram Hanya Hari
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Alhazan da suka hada da wakilan hukumar alhazai, jami’an hukumar jin dadin alhazai ta jiha, malamai, da sauran alhazai, sun bayyana jin dadinsu ga gwamnati da hukumar alhazai bisa irin kulawar da suka samu a lokacin aikin hajjin.
Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan isowar mahajjatan, babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa, Ahmed Labbo ya bayyana jin dadinsa bisa nasarar da aka samu na dawo da alhazan jihar Jigawa Nijeriya cikin koshin lafiya.
“Mun gode wa Allah da ya dawo mana da alhazan mu lafiya,” in ji Labbo.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp