HausaTv:
2025-11-27@21:17:18 GMT

Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka

Published: 17th, May 2025 GMT

Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta bayyana cewa babu wata rubutaciyar shawara data samu daga Amurka.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya musanta ikirarin samun rubutaccen sako daga Amurka kan yarjejeniyar nukiliya.

“Iran ba ta sami wata rubutacciyar shawara daga Amurka ba, kai tsaye ko a kaikaice,” in ji Araghchi a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Juma’a.

Wannan matsayi na zuwa ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi ikirarin cewa Iran ta samu wata shawara daga kasarsa.

Ya kara da cewa sakonnin da muke samu, kamar wanda duniya ke samu, suna cike da rudadi da kace-nace.

Amma matsayin Iran, na daram kuma babu ja da baya, ‘’ ku amince da hakkinmu ku kum akawo karshen takunkumai, idan hakan ya samu to za’a iya cimma matsaya.

Ministan hakokin wajen kasar ta Iran, ya kuma kara da cewa babu wani abu da zai sa Iran ta dakatar da hakkinta na inganta sanadarin uranium na zaman lafiya  ba wanda yake kunshe a cikin ‘yancin da aka baiwa dukkan kasashen da suka sanya hannun kan yarjejeniyar hana yaduwar makamman nukiliya.

A koyaushe muna maraba da tattaunawa bisa mutunta juna, sannan muna watsi da duk wani yunkuri na tilastawa ko matsin lamba. »

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon

Wani mai magana da yawun rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya (UNIFIL) ya tabbatar da cewa Isra’ila ta gina katanga kan iyakar da ta ratsa zuwa cikin yankin kasar Lebanon kusa da garin Yaroun, abin da tawagar ta bayyana a matsayin keta kudurin Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 1701.

“Isra’ila ta shafe shekaru da dama tana gina katanga a gefen Layin da aka Shata da ya raba yankunan Falastinu da Isra’ila ta mamaye da Lebanon, amma a cikin wannan yanayi katangar Isra’ila ta ratsa layin da ya raba bangarorin biyu,” in ji mai magana da yawun UNIFIL. “Don haka muna nuna rashin amincewa da wannan mataki, Wannan, a bayyane ya keta kuduri mai lamba 1701 da kuma hurumin kasar  Lebanon.” Inji shi.

Dakarun Masu Sanya ido kan zaman lafiya a kudancin kasar Lebanon UNIFIL  sun yi nazarin wurin kuma kuma tabbatar da cewa katangar ta ketare Layin da aka shata.

A cewar UNIFIL,  sun gano cewa katangar tana cikin kasar Lebanon kuma ta  kai  kimanin mita murabba’i 4,000 a cikin kasar Lebanon”.  Mai magana da yawun rundunar ya kara da cewa, tawagar ta sanar da sojojin na Isra’ila a hukumance  game da keta dokar da suka yi, inda suka mayar da martanin cewa za su dubi lamarin.

UNIFIL ta jaddada cewa za ta ci gaba da bin diddigin lamarin, da kuma ci gaba da Magana tare da dukkan bangarorin da abin ya shafa don tabbatar da cewa an kiyaye doka da kuma yin aiki da kudiri mai lamba 1701.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru  Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi