Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka
Published: 17th, May 2025 GMT
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta bayyana cewa babu wata rubutaciyar shawara data samu daga Amurka.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya musanta ikirarin samun rubutaccen sako daga Amurka kan yarjejeniyar nukiliya.
“Iran ba ta sami wata rubutacciyar shawara daga Amurka ba, kai tsaye ko a kaikaice,” in ji Araghchi a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Juma’a.
Wannan matsayi na zuwa ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi ikirarin cewa Iran ta samu wata shawara daga kasarsa.
Ya kara da cewa sakonnin da muke samu, kamar wanda duniya ke samu, suna cike da rudadi da kace-nace.
Amma matsayin Iran, na daram kuma babu ja da baya, ‘’ ku amince da hakkinmu ku kum akawo karshen takunkumai, idan hakan ya samu to za’a iya cimma matsaya.
Ministan hakokin wajen kasar ta Iran, ya kuma kara da cewa babu wani abu da zai sa Iran ta dakatar da hakkinta na inganta sanadarin uranium na zaman lafiya ba wanda yake kunshe a cikin ‘yancin da aka baiwa dukkan kasashen da suka sanya hannun kan yarjejeniyar hana yaduwar makamman nukiliya.
A koyaushe muna maraba da tattaunawa bisa mutunta juna, sannan muna watsi da duk wani yunkuri na tilastawa ko matsin lamba. »
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp