Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure
Published: 17th, May 2025 GMT
Hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano, ta dakatar da dukkanin cibiyoyin gudanar da taro da ke faɗin jihar, tare da haramta gudanar da bikin ‘Kauyawa Day’ gaba ɗaya.
Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne, ya bayyana hakan a ranar Asabar, bayan wata ganawa da masu ruwa da tsaki a jihar.
ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Borno Budurwa ta guntule mazakutar saurayinta da cizo a RibasYa ce wannan mataki na cikin sabuwar doka da majalisar dokokin Jihar Kano ta amince da ita, kuma Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanya wa hannu.
“Daga yanzu, duk wanda ya shirya wani taro da sunan Kauyawa ko Villagers Day, ya karya doka,” in ji El-Mustapha.
Sabuwar dokar ta bai wa hukumar ikon sanya ido da kula da dukkanin cibiyoyin taro da ayyukan DJ a jihar.
Saboda haka ne aka dakatar da dukkanin cibiyoyin taro har zuwa wani lokaci.
An ɗauki wannan mataki ne bayan ƙorafe-ƙorafe daga wasu ƙungiyoyin addini da na al’adu kan yadda ake gudanar da bikin Ƙauyawa Day.
Galibin waɗannan bukukuwa matasa da ’yan mata ne ke shirya su, amma ana zargin suna haifar ɗabi’un da ba su dace ba.
El-Mustapha, ya buƙaci shugabannin al’umma da jami’an tsaro su taimaka wajen tabbatar da wannan doka.
“Muna roƙon sarakunan gargajiya, ‘yan sanda, Hisbah da masu tsaron unguwanni su haɗa kai da mu wajen tabbatar da bin wannan umarni,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnatin Kano umarni
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Idris ya jaddada cewa Gwamnatin Tinubu tana da ƙudirin kare ’yancin faɗin albarkacin baki da ’yancin kafafen yaɗa labarai, waɗanda ya ce su ne ginshiƙan dimokiraɗiyya a ƙasar nan.
Ya ce: “Na bayyana ra’ayi na ga Jakaden, kuma na kuma jaddada ƙudirin gwamnati na ci gaba da kare ’yancin faɗin albarkacin baki da kuma rashin takura wa ‘yan jarida wajen gudanar da aikin su. Za mu ci gaba da kare wannan.
“Muna ganin aikin jarida da kafafen yaɗa labarai wani muhimmin ɓangare ne na dimokiraɗiyya.
“Babu wata dimokiraɗiyya da za ta yi nasara ba tare da kafafen yaɗa labarai ba.”
Sai dai kuma ministan ya buƙaci ‘yan jarida da su riƙa amfani da ‘yancin da suka samu cikin ƙwarewa da nuna kishin ƙasa.
Ya ce: “Muna kuma amfani da wannan dama wajen ƙarfafa gwiwar ‘yan jarida a Nijeriya cewa yayin da suke amfani da ’yancin kafafen yaɗa labarai, su tabbata suna ɗaukar nauyin aikin da muhimmanci.
“Su ci gaba da kasancewa masu sanin hakki, kuma a gaskiya sun kasance, amma muna buƙatar su ƙara jajircewa wajen yaɗa sahihan labarai da nuna kishin ƙasa, domin hakan ne kaɗai zai tabbatar da ɗorewar dimokiraɗiyyar.”
Ministan ya tabbatar da ci gaba da inganta wayar da kan jama’a kan kafafen yaɗa labarai da bayanai domin daƙile yaɗuwar labaran ƙarya.
A nasa ɓangaren, Jakaden Amurka, Mista Mills, ya ce ganawar sa da ministan ta kasance mai amfani matuƙa, musamman dangane da ’yancin kafafen yaɗa labarai da kuma sake duba Dokar Laifukan Intanet.
Ya ce: “Na yi wata muhimmiyar ganawa da Minista dangane da ’yancin kafafen yaɗa labarai a Nijeriya da kuma ƙudirin sa na kare wannan dama da ke bai wa mutane damar faɗin albarkacin bakin su.
“Na yaba da jawabin da ya fitar a ranar 3 ga Mayu, wato ranar ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai ta Duniya, inda ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na kare wannan ’yanci.
“Mun kuma tattauna batun sake fasalin Dokar Laifukan Intanet da kuma yadda na buƙaci cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta taka muhimmiyar rawa a cikin wannan sauyi a Majalisar Dokoki.”
Wannan shi ne karo na biyu da Jakaden Amurkan ya gana da Ministan kan batutuwan da suka shafi ’yancin kafafen yaɗa labarai a Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp