Aminiya:
2025-08-15@22:14:47 GMT

Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas

Published: 17th, May 2025 GMT

Aƙalla mutum biyar ne sun jikkata bayan da gobara ta tashi a gidan man Nobpet da ke kusa da mahaɗar Sojojin Sama a garin Fatakwal, Jihar Ribas.

Gobarar ta kuma ƙone sama da motoci takwas da aka ajiye kusa da ofishin Hukumar Sufuri ta Jihar Ebonyi.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba  Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro

Ma’aikatan kashe gobara na Jihar Ribas tare da haɗin gwiwar na Sojojin Sama ne suka yi aiki tare har suka iya kashe gobarar.

Ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, Emmanuel Ninyaegwu, wanda direba motar haya ne, ya ce motarsa mai ɗaukar fasinja 18 ta ƙone gaba ɗaya.

Ya kuma ce shi da matarsa mai ɗauke da juna biyu sun kuɓuta da ƙyar daga gobarar.

“Na shirya domin ɗaukar fasinjoji zuwa Jihar Ebonyi. Ina buɗe but ɗin motata sai na ji ƙarar gobara.

“Nan take na kwanta a ƙasa, na tashi da sauri na gudu kafin fashewar. Motata ta ƙone, wasu mutane sun jikkata, ni ma na samu rauni.

“Amma cikin ikon Allah babu wanda ya rasa ransa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa motar asibiti ta Sojojin Sama ta zo, inda aka dinga kula da waɗanda suka jikkata, sannan aka ɗauki wasu zuwa asibiti.

A cewarsa jami’an kashe gobara sun isa wajen amma ruwansu ya ƙare, sai da Sojojin Sama suka kai ɗauki sannan suka iya kashe wutar gaba ɗaya.

Wani wanda abin ya shafa, Anthony Ofoke, wanda shi ne mai kula da ayyukan Hukumar Sufuri ta Jihar Ebonyi a Jihar Ribas, ya ce gobarar ta lalata motocinsu guda biyu.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Jihar Ribas

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

Hukumar kula da kumbuna ta kasar Sin ta ce nan ba da jimawa ba, ‘yan sama jannatin kumbon Shenzhou-20 dake cibiyar binciken sararin samaniya ta kasar, za su gudanar da zagaye na 3 na ayyuka a wajen cibiyar.

‘Yan sama jannatin 3 da suka hada da Chen Dong da Chen Zhongrui da Wang Jie, sun gudanar da irin wannan aiki har sau biyu, a watannin Mayu da Yuni.

Baya ga haka, sun kammala ayyukan nazarin muhalli da kula da tantance da kayayyakin aiki a cikin cibiyar da jigilar kayayyaki. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • An Gano Gawar Wani Sojan HKI Wanda Ya Kashe Kansa Saboda yakin Gaza
  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
  • Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
  • ’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16