HausaTv:
2025-05-16@16:48:50 GMT

HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba

Published: 16th, May 2025 GMT

Majiyar kiwon lafiya a zirin Gaza ta bayyana cewa daga safiyar jiya Alhamis zuwa karfe 12 dare HKI ta kashe falasdinawa 143 tare da amfani da jiragen saman yaki tankunan yaki ta kasa da kuma jiragen ruwa yaki.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa bayan tsakiyar dare ma sojojin yahudawan sun kashe wasu karin mutane 21 wato a safiyar yau Jumma’a, a sansanin yan gudun hijira na Jabaliya.

wato sa’o’ii 5 bayan tsakiyar dare a kuma lokacin bada wannan labarin.

Labarin ya kara da cewa a wasu hare haren guda biyu a Khan Yunus sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 5 wasu daga cikinsu yara.

Gwamnatin Hamas a Gaza, ta bayyana cewa, tun lokacinda sojojin yahudawan suka sake komawa yaki a ranar 18 ga watan Maris da ya gabata sun kashe Falasdinawa 2,876.

Sannan tun daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 kuma ya kai mutane 56,000.

Jiya Alhamis ce ranar Nakba ga falasdinawa sabo ranarce aka kori falasdinawa daga kasarsu aka kuma kafa HKI.

A bangaren yahudawan sahyoniyya kuma wannan rana ce ta farinciki a tsakaninsu don aranar ce aka kafa HKI.

Mai yuwa shi ya sa sojojin yahudawan suka kara yawan kashe falasdinawa don kara masu bakinciki a wannan ranar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kashe falasdinawa sojojin yahudawan

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo

A ranar Asabar ne Shugaban Najeriya  Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Rome na ƙasar Italiya bisa gayyatar da sabon Fafaroma Leo XIV ya aike masa.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya sanar da cewa, shugaba Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariƙar Katolika na Najeriya domin halartar bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267.

Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno

A cewar Onanuga, Cardinal Pietro Parolin ya aike da goron gayyata daga Fafaroma Leo XIV, wanda ya ce bikin ya nuna “wani lokaci mai muhimmanci ga mabiyan Cocin Katolika da kuma duniya da ke fama da tashe-tashen hankula da rikice-rikice da dama”.

Fadar shugaban ƙasar ta ce cikin takardar gayyatar sabon fafaroman ya bayyana alaƙar ƙashin kai da Najeriya, yana mai cewa ”ƙasarka mai girma na da mutuƙar muhimmanci a gareni, saboda na yi aiki a majami’ar Apostolic Nunciature da ke birnin Lagos a shekarun 1980”.

A cewar sanarwar, tawagar ta shugaba Tinubu za ta haɗa da Minista a harkokin waje, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu; Archbishop Lucius Ugorji na Owerri da kuma shugaban rukunin Bishop na Katolika na Najeriya; Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja; da Alfred Martins na Legas; da kuma Bishop ɗin Katolika na Diocese na Sokoto, Mathew Hassan Kukah.

Fafaroma Leo XIV, tsohon Cardinal Robert Francis Prevost, za a rantsar da shi a matsayin Fafaroma a ranar Lahadi, 18 ga Mayu, a dandalin St Peter’s da ke Vatican.

Fafaroma Leo, wanda shi ne Fafaroma na farko daga Amurka an zaɓe shi ne kwanaki 17 bayan mutuwar magabacinsa, Fafaroma Francis, a ranar 21 ga Afrilu. Shi ne zai jagoranci Katolika biliyan 1.4 na duniya.

Ana sa ran shugaba Tinubu zai koma Abuja ranar Talata, 20 ga watan Mayu, in ji sanarwar

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo
  • Dubban Falasdinawa Sun Fito Kan Titunan NewYork Don Tunawa Da Ranar Musiba ko Nakba
  • Iran Tace Ranar Nakba Farawa Ce Na Musibu Ba Karshensu Ba
  • Kungiyar Hamas Ta Shirya Zanga-Zangar Goyon Bayan Halaccin Yunkurin ‘Yantar Da Kasarsu Daga Mamayar Yahudawa
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Sabon Hari: An kashe makiyaya 1 da shanu sama da 100 a Filato
  • Fiye Da Falasdinawa 80 Ne Su Ka Yi Shahada Daga Safiyar Yau Alhamis
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Gaza