HausaTv:
2025-08-15@08:03:05 GMT

HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba

Published: 16th, May 2025 GMT

Majiyar kiwon lafiya a zirin Gaza ta bayyana cewa daga safiyar jiya Alhamis zuwa karfe 12 dare HKI ta kashe falasdinawa 143 tare da amfani da jiragen saman yaki tankunan yaki ta kasa da kuma jiragen ruwa yaki.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa bayan tsakiyar dare ma sojojin yahudawan sun kashe wasu karin mutane 21 wato a safiyar yau Jumma’a, a sansanin yan gudun hijira na Jabaliya.

wato sa’o’ii 5 bayan tsakiyar dare a kuma lokacin bada wannan labarin.

Labarin ya kara da cewa a wasu hare haren guda biyu a Khan Yunus sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 5 wasu daga cikinsu yara.

Gwamnatin Hamas a Gaza, ta bayyana cewa, tun lokacinda sojojin yahudawan suka sake komawa yaki a ranar 18 ga watan Maris da ya gabata sun kashe Falasdinawa 2,876.

Sannan tun daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 kuma ya kai mutane 56,000.

Jiya Alhamis ce ranar Nakba ga falasdinawa sabo ranarce aka kori falasdinawa daga kasarsu aka kuma kafa HKI.

A bangaren yahudawan sahyoniyya kuma wannan rana ce ta farinciki a tsakaninsu don aranar ce aka kafa HKI.

Mai yuwa shi ya sa sojojin yahudawan suka kara yawan kashe falasdinawa don kara masu bakinciki a wannan ranar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kashe falasdinawa sojojin yahudawan

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina

Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da miƙa wa mataimakinsa, Malam Faruk Jobe, ragamar mulkin jihar, inda shi kuma zai tafi hutun mako uku domin duba lafiyarsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labaran jihar, Bala Salisu Zango, ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta bayyana cewa hutun zai fara ne daga ranar Litinin, 18 ga watan Agusta, 2025.

An zabi sabuwar firaminista a Luthuania Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC

A cewar Gwamna Radda, hutun zai ba shi damar samun kulawar likitoci da kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa cikin koshin lafiya.

“Cikin matakan da nake ɗauka don kula da lafiyata da kuma ganin na yi aiki cikin yanayi mai kyau, na ɗauki wannan matakin tafiya hutu, kuma zan dawo da zarar likitoci sun gama duba ni,” in ji gwamnan a cikin sanarwar.

A watan Yuli ne gwamnan ya gamu da hatsarin mota a kan hanyar Katsina zuwa Daura, lamarin da ya jawo damuwa a tsakanin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.