HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba
Published: 16th, May 2025 GMT
Majiyar kiwon lafiya a zirin Gaza ta bayyana cewa daga safiyar jiya Alhamis zuwa karfe 12 dare HKI ta kashe falasdinawa 143 tare da amfani da jiragen saman yaki tankunan yaki ta kasa da kuma jiragen ruwa yaki.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa bayan tsakiyar dare ma sojojin yahudawan sun kashe wasu karin mutane 21 wato a safiyar yau Jumma’a, a sansanin yan gudun hijira na Jabaliya.
Labarin ya kara da cewa a wasu hare haren guda biyu a Khan Yunus sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 5 wasu daga cikinsu yara.
Gwamnatin Hamas a Gaza, ta bayyana cewa, tun lokacinda sojojin yahudawan suka sake komawa yaki a ranar 18 ga watan Maris da ya gabata sun kashe Falasdinawa 2,876.
Sannan tun daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 kuma ya kai mutane 56,000.
Jiya Alhamis ce ranar Nakba ga falasdinawa sabo ranarce aka kori falasdinawa daga kasarsu aka kuma kafa HKI.
A bangaren yahudawan sahyoniyya kuma wannan rana ce ta farinciki a tsakaninsu don aranar ce aka kafa HKI.
Mai yuwa shi ya sa sojojin yahudawan suka kara yawan kashe falasdinawa don kara masu bakinciki a wannan ranar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kashe falasdinawa sojojin yahudawan
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.
Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.
Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.
DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar NejaWannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.
A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.
Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.
Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.
A watan Yuli 2025 Gwamna Umar Namadi ya gudanar da bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.
Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma samar da tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da zubar da jini.