Iran: Cikakken Goyon Bayan Amurka Ga ‘Yan Sahayoniya Ne Yake Sa Su Tafka Laifuka
Published: 16th, May 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriryar musulunci ta Iran ta sanar da cewa, saboda yadda Amurka take bai wa ‘yan sahayoniya cikakken goyon baya ne, ya sa su cigaba da aikata laifuka na kisan kiyashi akan mutanen Gaza.
Bayanin da ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta fitar, ya zo ne saboda tunawa da zagayowar lokacin da aka kori Falasdina aka kirkiri HKI, wanda ake kira da “Nakba” ta bayyana cewa; Falasdinawa ne suke da hakkin ayyana makomarsu,kuma nauyi ne na doka da halin kwarai akan kasashen duniya su takawa HKI birki akan kisan kiyashin da take yi a Gaza.
Bayanin ya sake jaddada kira da gabatar da masu hannu a kisan kiyashin al’ummar Gaza a gaban kotu domin su fuskanci sakamakon laifukan da su ka tafka.
Bayanin ya yi ishara da munin laifukan da ‘yan sahayoniyar suke tafkwa a Gaza, wanda ya shafi mata da kananan yara da ba su ji, ba su gani ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
Tsohon tauraron ƙungiyoyin Manchester United da Real Madrid, Ruud van Nistelrooy ya ajiye aikinsa na horas da Leicester City bisa fahimtar juna.
Wannan na zuwa ne bayan da a ƙarƙashin jagorancinsa ƙungiyar ta yi wasanni 27 da ta gaza taɓuka abin a zo a gani a cikinsu, lamarin da ya kai ta ga faɗawa gasa mai daraja ta biyu a Ingila wato Championship.
Wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta ce an cimma matsaya tsakaninta da Van Nistelroy ne bayan tattaunawar da suka yi.
A ƙarshen watan Nuwamban da ya gabata, bayan da ta kori Steve Cooper a lokacin da suke matsayi na 16 a gasar Firimiyar bara, Liecester City ta ƙulla yarjejeniya da Van Nistelrooy, kwangilar da ba za ta ƙare ba sai a shekarar 2027.
To amma duk da sauyin da aka samu kwalliya ta gaza biyan kuɗin sabulu domin kuwa a haka suka yi ta tafiya da ƙyar.
Daga ƙarshe ma dai ƙungiyar ta sha kashi da ci 1-0 a karawar ta Liverpool a ranar 20 ga watan Afrilu, rashin nasarar da ta tabbatar da cewar ƙungiyar ta yi adabo da gasar Firimiya sai kuma wani jiƙon.
A halin yanzu dai ana sa ran tsohon Kocin Burnley da Everton, Sean Dyche ya maye gurbin da Nistelrooy ya bari.