Iran: Cikakken Goyon Bayan Amurka Ga ‘Yan Sahayoniya Ne Yake Sa Su Tafka Laifuka
Published: 16th, May 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriryar musulunci ta Iran ta sanar da cewa, saboda yadda Amurka take bai wa ‘yan sahayoniya cikakken goyon baya ne, ya sa su cigaba da aikata laifuka na kisan kiyashi akan mutanen Gaza.
Bayanin da ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta fitar, ya zo ne saboda tunawa da zagayowar lokacin da aka kori Falasdina aka kirkiri HKI, wanda ake kira da “Nakba” ta bayyana cewa; Falasdinawa ne suke da hakkin ayyana makomarsu,kuma nauyi ne na doka da halin kwarai akan kasashen duniya su takawa HKI birki akan kisan kiyashin da take yi a Gaza.
Bayanin ya sake jaddada kira da gabatar da masu hannu a kisan kiyashin al’ummar Gaza a gaban kotu domin su fuskanci sakamakon laifukan da su ka tafka.
Bayanin ya yi ishara da munin laifukan da ‘yan sahayoniyar suke tafkwa a Gaza, wanda ya shafi mata da kananan yara da ba su ji, ba su gani ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda
Shirin zai kuma samar da dubban guraben aikin yi ga matasa, wanda hakan zai rage rashin aikin yi a ƙasar.
Mutanen karkara da manoma da suka fi fama da matsalolin tsaro za su fi amfana da wannan mataki.
Shugaba Tinubu ya jaddada cewa ba za a bar masu aikata laifuka suke cin karensu ba babbaka ba.
Ya ce gwamnati za ta wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ko ina a cikin Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp