Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriryar musulunci ta Iran ta sanar da cewa, saboda yadda Amurka take bai wa ‘yan sahayoniya cikakken goyon baya ne, ya sa su cigaba da aikata laifuka na kisan kiyashi akan mutanen Gaza.

Bayanin da ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta fitar, ya zo ne  saboda tunawa da zagayowar lokacin da aka kori Falasdina aka kirkiri HKI, wanda ake kira da “Nakba” ta bayyana cewa; Falasdinawa ne suke da hakkin ayyana makomarsu,kuma nauyi ne na doka da halin kwarai akan kasashen duniya su takawa HKI birki akan kisan kiyashin da take yi a Gaza.

Bayanin ya sake jaddada kira da gabatar da masu hannu a kisan kiyashin al’ummar Gaza a gaban kotu domin su fuskanci sakamakon laifukan da su ka tafka.

Bayanin ya yi ishara da munin laifukan da ‘yan sahayoniyar suke tafkwa a Gaza, wanda ya shafi mata da kananan yara da ba su ji, ba su gani ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Iran Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari

Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani da karfi kan duk wani wuce gona da iri kanta

Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya bayyana cewa: Gwagwarmaya ita ce babban jari kuma wata dabara mai kima ga yankin, yana mai jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani mai karfi kan duk wani hari da aka kai mata, kuma babu wata tattaunawa da za ta yi tasiri a karkashin tunanin Amurka na “zaman lafiya da nuna karfi.”

Ali Larijani ya jaddada a shirye Iran take a koda yaushe ta mayar da martani mai karfi kan duk wani hari da gwamnatin mamayar Isra’ila za ta kai kan kasar Iran, yana mai cewa “Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta bar yankin Gabas ta Tsakiya ya zauna lafiya ba, muddin Netanyahu na kan karagar mulki, ba zai bari al’amura su daidaita ba, ko da a Falastinu.”

Yana mai jaddada cewa; Netanyahu mugun mutum ne mai haifar da rikici don amfanin kansa.

A wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Al-Mayadeen, Larijani ya kara da cewa: “Benjamin Netanyahu mugun mutum ne kuma ba zai bari al’amura su daidaita ba, a kullum yana kai hari kan kasar Lebanon da ma wasu kasashe, domin daga hakula a kasashen, kuma an ga abin da ya yi a kasar Siriya, wannan hargitsin tsaro da yake haddasawa a kasashe abu ne da ba za a amince da shi ba.”

Hukumar yada labaran Isra’ila ta watsa rahoton cewa, tun farkon yakin Gaza, kimanin sojoji 3,770 ne aka tabbatar sun kamu da rashin lafiya kwakwalwa saboda da tashe-tashen hankula.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Human Rights Watch Ta Ce; Kai Hari Kan Gidan Yarin Evin Na Iran Laifin Yaki Ne August 15, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Wani Mummunan Hari Kan Gaza Tare Da Rusa Gidajen Mutane A Khan Yunis August 15, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza August 15, 2025 Gwamnatin Mali Ta Bankado Wata Makarkashiyar Janyo Hargitsi A Kasar Tare Da Wargaza Shi August 15, 2025 Iran: Suna Bukatar Kawo Karshen Makaman Nukiliya Da Kuma Furuci Maras Daɗin Ji August 15, 2025 Kungiyar Ansarullahi Ta Kasar Yemen Ya Ce; Yahudawan Sahayoniyya Suna Yakar Al’ummar Falasdinu Duka Ne August 15, 2025 Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza August 15, 2025 Laifukan Cin Zarafi Musamman Kisha Kiyashi A Kasar Siyasa Ya Doshi Laifukan Yaki August 15, 2025 Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan August 15, 2025 Miliyoyin Mutane Sun Taru A Karbala Don Juyayin 40 Na Shahadarsa Imam Hussain(a) August 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • China Tace Bata Goyon Bayan A Sake Dorawa Iran Takunkuman MDD
  • An Gano Gawar Wani Sojan HKI Wanda Ya Kashe Kansa Saboda yakin Gaza
  • Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Iran Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • ‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Ƙudiri – Kamfani.
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse
  • Hamas ta aike da wasikar yabo ga Yemen kan goyon bayan Gaza
  • Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran