A kokarin da yake yi na jigilar maniyyatan aikin hajjin bana, Kamfanin jiragen sama na Max Air yace zai kwashe daukacin Alhazan Jihar Jigawa cikin kwanaki biyu.

 

Mataimakin mai kula da ofishin kamfanin dake jihar kano, Mr Barnabas Anderson ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shelkwatar hukumar Jin dadin alhazan jihar Jigawa dake Dutse babban birnin jihar.

A cewarsa, ana sa fara jigilar maniyatan jihar  zuwa kasar Saudi Arabia a ranar 20 da kuma 21 ga watan Mayun 2025.

 

Ya ce jirgin Max air zai yi sawun farko da maniyata su 550 zuwa kasa mai tsarki a ranar 20 ga watan Mayu.

 

Mr Anderson yace a ranar 21 kuma, jirgi na biyu zai dauki maniyata 400 zuwa kasar Saudi Arabia.

Yayi nuni da cewar,jami’an kamfanin za su iso Dutse a ranar 19 ga wata domin kammala duk wani shiri na jigilar maniyatan.

 

Ya kuma ce kamfanin max air zai tabbatar da ganin an yi jigilar maniyatan cikin kwanciyar hankali domin sauke nauyin da aka dora masa.

 

Shi ma a nasa jawabin, wakilin hukumar aikin hajji ta kasa mai kula da jihohin Kano da Jigawa, Alhaji Salisu Gaya ya ce hukumar za ta tabbatar da ganin an yi jigilar maniyatan Jihar Jigawa cikin tsari.

A don haka, ya kuma bukaci maniyyatan da su kiyaye da ka’idoji da kuma dokokin kasa mai tsarki domin kare kima da kuma martabar kasa Najeriya.

 

A jawabinsa, Darakta Janar na hukumar Jin dadin alhazan jihar jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo yace hukumar ta raba dukkannin kayayyakin aikin hajji ga maniyyata ta hannun shugabannin shiyya-shiyya na hukumar.

 

Ya kara da cewar, hukumar ta kuma kammala aiki akan takardun biza na maniyyata da yi musu allurar rigakafi da kuma tanadin kudaden guzuri wato BTA.

Alhaji Ahmed Umar Labbo yace makasudin gudanar da taron masu ruwa da tsakin shi ne, domin bibiyar shirye-shiryen da suka yi na samun nasarar aikin hajjin bana dake tafe.

 

Labbo, ya kuma bayyana cewar, hukumar ta biya bashin naira miliyan dubu 3 da miliyan 360 da Gwamnatin jihar ta bata rance domin sayen kujerun aikin hajjin bana.

 

Ya Kara da cewar, rancen kudin ya  matukar taimakawa hukumar wajen tare kujerun maniyyatan jihar a hukumar aikin hajji ta kasa wato NAHCON.

 

Kazalika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa hadin kai da goyon bayan da yake baiwa hukumar a kowanne lokaci.

 

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa jigilar maniyatan jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Kaduna Tace Zuba Jarin Da Ta Yi Na Euro Miliyan Dari Da Shadaya Zai Maganin Sufuri A Jihar

 

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce zuba jarin Euro miliyan dari da goma sha ɗaya da tayi akan aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani zai rage cunkoson ababen hawa da kuma inganta rayuwar al’ummar jihar.

 

Kwamishinan Ma’aikatar Ayyuka da Ababen More Rayuwa ta Jihar Kaduna, Ibrahim Hamza, ne ya bayyana hakan a taron masu ruwa da tsaki kan aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani wato BRT da aka gudanar a Kaduna.

 

Aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani yana da nufin inganta zirga-zirgar ababen hawa a birane, rage cunkoso, da kuma inganta rayuwar jama’ar Jihar Kaduna.

Kwamishina Ma’aikatar Aiyyuka da Ababen More Rayuwa, Ibrahim Hamza ya tabbatar da kudurin gwamnati na sauya fasalin harkar sufuri da nufin ƙara bunƙasa tattalin arziki da jin daɗin al’umma.

 

Ya bayyana cewa aikin BRT wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati na inganta harkokin sufuri a faɗin jihar.

 

A nasa jawabin, Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna, Injiniya Inuwa Ibrahim, ya ce tsarin BRT wani babban ci gaba ne wajen magance matsalolin sufuri da ke addabar yawan jama’a.

 

Ya kuma shawarci mahalarta taron su yi nazari mai zurfi kan matsalolin da ake fuskanta tare da samar da mafita domin sauƙaƙa rayuwar fasinjoji.

 

A nasa ɓangaren, jagoran ƙungiyar Rebel Artic Joint Venture, Ted Regino, ya bayyana cewa kamfaninsu ne ke da alhakin kula da masu aikin, inda ya tabbatar wa al’ummar Kaduna da ingantaccen aiki mai sauri da nagarta.

 

Mai Kula da wannan taron Injiniya Emmanuel Oche John, ya ce suna tabbatar da cewa dukkan masu ruwa da tsaki sun samu cikakken bayani kan aikin.

 

Wani mahalarta taron, Shugaban Ƙungiyar Masu Motocin Haya ta Ƙasa reshen Jihar Kaduna (NARTO), Alhaji Babangida Jafaru, ya bayyana cewa aikin BRT zai taimaka wajen warware matsalolin sufuri da ake fama da su a jihar.

Taken taron shi ne: “BRT a matsayin Kayan Aiki don Sarrafa Yawan Jama’a cikin Dorewa a Zamanin Fasaha,” inda aka gayyato wakilai daga NURTW, FRSC, KASTELEA da sauransu.

 

Cov/Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka
  • NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa
  • Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko
  • Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kudirin Dokar Hukumar Kula Da Manyan Makarantun Sakandire
  • NUJ Jigawa Ta Nada Wakilin Rediyon Tarayya A Matsayin Mamba Na Musamman
  • Gwamnati Kaduna Tace Zuba Jarin Da Ta Yi Na Euro Miliyan Dari Da Shadaya Zai Maganin Sufuri A Jihar
  • Dole Ne Kansiloli Su Shiga Cikin Dukkan Ayyukan Kananan Hukumomin Su – Gwamna Yusuf