A kokarin da yake yi na jigilar maniyyatan aikin hajjin bana, Kamfanin jiragen sama na Max Air yace zai kwashe daukacin Alhazan Jihar Jigawa cikin kwanaki biyu.

 

Mataimakin mai kula da ofishin kamfanin dake jihar kano, Mr Barnabas Anderson ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shelkwatar hukumar Jin dadin alhazan jihar Jigawa dake Dutse babban birnin jihar.

A cewarsa, ana sa fara jigilar maniyatan jihar  zuwa kasar Saudi Arabia a ranar 20 da kuma 21 ga watan Mayun 2025.

 

Ya ce jirgin Max air zai yi sawun farko da maniyata su 550 zuwa kasa mai tsarki a ranar 20 ga watan Mayu.

 

Mr Anderson yace a ranar 21 kuma, jirgi na biyu zai dauki maniyata 400 zuwa kasar Saudi Arabia.

Yayi nuni da cewar,jami’an kamfanin za su iso Dutse a ranar 19 ga wata domin kammala duk wani shiri na jigilar maniyatan.

 

Ya kuma ce kamfanin max air zai tabbatar da ganin an yi jigilar maniyatan cikin kwanciyar hankali domin sauke nauyin da aka dora masa.

 

Shi ma a nasa jawabin, wakilin hukumar aikin hajji ta kasa mai kula da jihohin Kano da Jigawa, Alhaji Salisu Gaya ya ce hukumar za ta tabbatar da ganin an yi jigilar maniyatan Jihar Jigawa cikin tsari.

A don haka, ya kuma bukaci maniyyatan da su kiyaye da ka’idoji da kuma dokokin kasa mai tsarki domin kare kima da kuma martabar kasa Najeriya.

 

A jawabinsa, Darakta Janar na hukumar Jin dadin alhazan jihar jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo yace hukumar ta raba dukkannin kayayyakin aikin hajji ga maniyyata ta hannun shugabannin shiyya-shiyya na hukumar.

 

Ya kara da cewar, hukumar ta kuma kammala aiki akan takardun biza na maniyyata da yi musu allurar rigakafi da kuma tanadin kudaden guzuri wato BTA.

Alhaji Ahmed Umar Labbo yace makasudin gudanar da taron masu ruwa da tsakin shi ne, domin bibiyar shirye-shiryen da suka yi na samun nasarar aikin hajjin bana dake tafe.

 

Labbo, ya kuma bayyana cewar, hukumar ta biya bashin naira miliyan dubu 3 da miliyan 360 da Gwamnatin jihar ta bata rance domin sayen kujerun aikin hajjin bana.

 

Ya Kara da cewar, rancen kudin ya  matukar taimakawa hukumar wajen tare kujerun maniyyatan jihar a hukumar aikin hajji ta kasa wato NAHCON.

 

Kazalika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa hadin kai da goyon bayan da yake baiwa hukumar a kowanne lokaci.

 

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa jigilar maniyatan jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna

Wata ’yar kasuwa mai taimakon al’umma, Barista Catherine Bitrus, ta raba wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura, a Jihar Kaduna.

Tallafin ya haɗa da injinan niƙa, buhunan shinkafa, katan-katan na taliyar yara, da man girki.

Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima

A lokacin rabon kayan, Catherine, shugabar kamfanin Natural Beauty Secret, ta ce ta yi hakan ne domin taimaka wa matan karkara da ke fama da matsaloli a rayuwa.

“Allah Ya ba ni arziƙi, shi ya sa na ga dacewa na raba da waɗanda ke bukata,” in ji ta.

“Na zaɓi mata ne domin na san irin wahalar da suke sha.”

Ta roƙi matan da su dage da ƙoƙari, ka da su yanke ƙauna, domin komai na duniya yana da mafita idan aka jajirce.

Catherine ta ce tana da niyyar ci gaba da wannan aiki, kuma ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, saboda irin goyon bayan da yake bai wa mata a jihar.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Barista James Kanyip, ya yaba da wannan aiki, inda ya buƙaci sauran masu hali da ƙungiyoyin su dinga tallafa wa marasa ƙarfi.

Shugaban kwamitin shirya taron, Lucky Ezra, ya bayyana Catherine a matsayin mace mai zuciyar taimako da kishin jama’a.

A madadin sauran matan da suka amfana, Josephine Bature ta nuna farin ciki da godiya, tare da addu’ar Allah Ya saka wa Catherine da alheri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake
  • Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
  • Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Mutane 1
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
  • Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga