Harajin ya kuma kai kasa da kimanin kaso 11 a cikin dari, wanda ya kai kasa da wanda ake karba, idan aka kwatanta da duniya.

“Abinda muka yi shi ne, mun cire daukacin ma’aikatan da karbar kasa kaso uku a cikin darei a cikin tsarin na karabar harajin,” Inji tsohon Shugaban LLP.

Ya shedawa manyan Malaman Makaranta  da Jami’an da ke katbar haraji hakan ne, a wani taro da aka gudanar a jihar Legas

Nijeriya dai, ta kasance kasar da sama da alumominta miliyan 8o, ke fama da kangin talauci.

Hakan ya kuma kara haifar da hauhawan farashin kayan masarufi, musamman yadda kayan suka tashi a 2024, kafin su sauka zuwa kaso 24.2 a cikin dari.

Kazalika, hauhauwan farashi da sauye-sauyen da gwamnatin kasar ta kirkiro da su da cire tallafin Man Fetur da kuma faduwar darajar Naira, sun sanya kudaden shigar da ake samu a kaar, sun ragu.

An dai yiwa fasalin dokar karbar haraji kai da kai ne a kasar ne na karshe a  2011 a yayin da wasu ‘yan kasar, ke samun kudin shiga a duk shekara da suka kai Naira 3.6 a wancan lokacin.

Oyedele ya ci gaba da cewa, sai dai, a yanzu, an, na  samun kudin shiga da suka kai kasa da Naira miliyan 1.7 a duk wata wanda suka kai daidai da dala 1,060.

Ana sa ran wannan Kwamtin, zai saita dokokin na karbar harajin, a zango na karashen na 2026.

Ana kuma sa ran, za daga kimar karbar harajin da ga wanda ake da shin a yanzu, na kaso 7.5 a cikin dari, zuwa kaso 10 a cikin dari, a 2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Haraji a cikin dari

এছাড়াও পড়ুন:

Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi

Tsohon Gwamnan Anambra, Peter Obi ya ce zai yi takarar shugabancin Nijeriya a 2027 domin ba zai shiga duk wata yarjejeniyar haɗakar takara da kowa ba.

Obi wanda ya yi takarar shugabancin Nijeriya a Zaben 2023 a karkashin inuwar jam’iyyar Labour (LP), ya tabbatar wa magoya bayansa cewa babu gudu babu ja da baya dangane da takararsa a babban zaɓen kasar na gaba.

An sanya dokar hana fita a Kaduna An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Sai dai ya ce idan har akwai wata yarjejeniya da zai kulla, ba za ta wuce wacce za ta ba shi damar zama shugaban ƙasa na wa’adi daya ba, sannan ya miƙa wa shugaba na gaba mulki a ranar 28 ga watan Mayun 2031.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya fitar, Obi ya bayyana hakan a yayin amsa tambayoyin magoya bayansa  wata hira ta kai tsaye da aka yi da shi a shafin X a ranar Lahadi.

Obi ya musanta kulla yarjejeniyar tsayawa takara a karkashin tikiti daya da tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar.

Haka kuma, Obi ya ce duk wata haɗaka da za a yi wadda ba ta da kudirin kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihohin Benuwe da Zamfara…da kuma bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, to kuwa babu shi babu ita.

Kazalika, Obi ya ce yana goyon bayan tsarin da zai bayar da damar a rika karɓa-karɓar mulki a tsakanin Kudu da Arewacin Nijeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi
  • Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Yin Kutse Cikin Yankunan Kasar Siriya
  • Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
  • Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
  • Har yanzu mun gaza gano dalilin ɓullar COVID-19 — WHO
  • Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  • Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva