Aminiya:
2025-08-15@19:09:28 GMT

Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe

Published: 16th, May 2025 GMT

Wani rikici da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyen Chikuriwa da ke Ƙaramar Hukumar Nangere a Jihar Yobe, ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata wasu.

Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, 13 ga watan Mayu, 2025 bayan da wani makiyayi ya shigar da shanunsa cikin gonar wani manomi, abin da ya tayar da rikici.

Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa

A lokacin da rigimar ta ɓarke, an harbi wani manomi mai suna Babayo Maina Osi da kibiya a goshinsa, wanda hakan ya jikkata shi.

Wata majiya daga ƙauyen ta ce rikicin ya ƙazanta sosai har ya rikiɗe zuwa faɗa tsakanin manoma da makiyaya.

A lokacin wannan faɗa ne aka harbi wani mutum mai suna Usman Mohammed, mai shekara 35 da kibiya, wanda daga bisani ya rasu a Babban Asibitin Nangere.

Jami’an tsaro sun isa wajen domin daƙile rikicin da kuma hana ya ƙara rincaɓewa.

Rahoton ya bayyana cewa an ƙwato shanu biyu, awaki 29 da raguna daga hannun manoman da ake zargi sun ƙwace daga hannun makiyaya.

A yanzu haka, an gayyaci shugabannin ɓangarorin biyu domin tattaunawa da kuma tabbatar da cewa irin wannan rikici bai sake faruwa ba a nan gaba.

Duk ƙoƙarin da wakilin Aminiya ya yi don jin ta bakin kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Dungus Abdulkareem, ya ci tura, domin bai daga wayarsa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

A farkon wannan shekarar da ta gabata, Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, a wani taro ya bai wa kungiyoyin na Sufurin Jiragen Sama tabbacin cewa, Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da bi ka’ida wajen sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman kasa.

Keyamo ya kuma bai wa shugabannin kungiyoyin tabacin cewa, suma a sanya kan batun na yarjejeniyar ta sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman.

Kazalika, ba su tabbacin cewa, zai umarci hadiminsa domin ya ci gaba da sanar da shugabannin kungiyoyin kan abinda ke tafiya game da yarjejeniyar.

Sai dai, a jawabin da shuwagabbin kungiyar da kuma na ma’aikatan suka gabatar a wani babban taronsu a shalakwar Tashar Jiragen Sama da ke a jihar Legas, sun soki Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, bisa zagaye shugabannin kungiyoyin kan batun na jarjejeniyar.

A jawabinsa shugaban kungiyar ma’aikatan zirga-zirga ta jiragen sama na kasa NUATE Kwamarade Ben Nnabue ya yi kira da sake sabon lale kan batun na yarjeniyar musamman domin a bai wa sauran masu ra’ayin shiga cikin yarjejeniyar.

“Ya kamata a sake faro yarjejeniyar tun daga farkonta, domin a bai wa sauran ‘yan Nijeriya damar shiga cikin yarjejeniyar,”Inji Shugaban.

Nnabue ya ci gaba da cewa, a matsayinsu na shuwagabannin kungiyoyin sam ba su da wata masaniya game da wannan yarjejiniyar da da Gwamnatin ta kulla.

Ya kara da cewa, hatta shuwagabannin kungiyoyin kwadago ba a sanar da su, game da yarjejiniyar ba, amma sai kawai muka ji, Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, sanar da cewa, Majalisar Zartwar kasar ta amince da wannan yarjejeniyar, musamman ta Tashar Jirgin Sama na jihar Enugu.

“Muna son mu sanar da duniya cewa, dole kafin a gudanar da duk wata yarjejniya a fara tattaunawa da shuwagabbin kungiyoyin kwadago tukunna, ” A cewar Kwamarade Ben.

Ya sanar da cewa, hanyoyin da ake bi na gudanar da wannan yarjejeniyar, cike take da kura-kurai domin ba mu da wata masaniya ko an bayar da talla ga manyan Jaridun kasar nan kan batun na yarjeniyar.

“Tashoshin Jiragen Sama na kasar nan, mallakin ‘yan Nijeriya, a saboda haka ba za ta sabu kawai a cikin dare daya mu ji an yanke shawarar cewa, akwai wasu ‘yan lele da ake so su kadai a yi yarjejeniyar da sub a, domin kamata ya yi ba bar abin a bude domin suma ‘yan kasar, su gyada ta su sa’ar, a saboda haka, muna bukatar a soke wannan yarjejniyar har sai idan an bi ka’idar da ta dace, “ Inji shugaban.

Shi ma a na sa bangaren shugaban kungiyar kwarru ta ANAP Kwamarade Alale Adedayo, ya yi tir da hanyoyin da Ministan ya bi domin yin wannan yarjejeniyar ba tare da janyo shugabannin kungoyoyin ba kamar yadda ya yi masu alkwari a baya.

Kwamarade Adedayo ya bukaci da sake sabon lale kan batun wannan yarjejeniyar, musamman domin a tabbatar da an bi ka’aida da kuma yin gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 
  • ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • ‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi
  • Fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin Keffi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto