Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa
Published: 16th, May 2025 GMT
Da safiyar yau Juma’a ne dai jami’an tsaron kasar Chadi su ka kai wani farmaki na kama tsohon fira minista kuma jagoran ‘yan hamayyar siyasar kasar Succès Masra.
Jam’iyyar hamayya da Masra yake jagoranta, ta bayyana abinda jami’an tsaron su ka yi wa jagoran nata da cewa, garkuwa ce.
Ita kuwa hukumar kasar ba ta fitar da wani bayani akan kamun Masra ba,wanda shi ne ya zo na uku a zaben shugaban kasar da aka gudanar a shekarar da ta gabata.
Bayanin da jam’iyyar adawar ta masu; Sauyi” ta wallafa a shafinta na ‘facebook’ ya kunshi cewa; shugaba Succes Masra an yi garkuwa da shi da karfin bindiga da safiyar yau 16 ga watan Mayu da misalign karfe; 05; 56 daga gidansa da yake kusa da babbar cibiyar jam’iyyar.
A karkashin sanarwar, Shafin jam’iyyar na ‘facebook’ an kuma wallafa hoton bidiyo na shugaban jam’iyyar yana fitowa daga gidansa zagaye da masu dauke da makamai da suke sanye da kakin soja.
Babban mai shigar da kara na kasar ta Chadi Umar Muhammad Kidilayi ya fada wa kamfanin dillancin labarun Faransa cewa lallai an kama Masra.
Masra dan shekaru 41 ya rike mukamin Fira ministan kasar na tsawon watanni 5 gabanin zaben shugaban kasar da aka yi a watan Mayu na 2024.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
Wata kotun tarayya a kasar Kanada ta ayyana manyan jam’iyyun Najeriya na APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci yayin da ta hana wani tsohon dan siyasa, Douglas Egharevba, mafaka a kasar saboda alakarsa da jam’iyyun.
Jaridar Peoples Gazette ta rawaito cewa alkalin kotun, Phuong Ngo, a hukuncin da ta yanke ranar 17 ga watan Yunin 2025, ta hana dan siyasar izinin shiga kasar bayan samun shi da gaza cika sharudan dokar shige da fice ta kasar.
A cewar alkalin, “Dabi’ar wasu ’yan siyasa ’yan PDP, wadanda wasu daga cikinsu ma kusoshi ne a jam’iyyar, da wadanda suka aikata laifukan siyasa ko aka yi da yawunsu, ta yi yawan da ba zai yiwu a ki alakanta shugabancin jam’iyyun da ita ba.”
Ana sa ran dai nan ba da jimawa ba gwamnatin Najeriya za ta fitar da sanarwa kan matsayinta a hukumance, kamar yadda wani babban jami’in gwamnati ya tabbatar mana, yana mai bayyana hukuncin a matsayin abin takaici.
Ita kuwa jam’iyyar PDP, ta bakin mamba a kwamitinta na zartarwa, Timothy Osadolor, ta ce kotun na da ’yancin fadin albarkacin bakinta, amma hukuncin nata ba yak an gaskiya.
“Amma babu wata hujja a cikin ra’ayin nasu da zai sa dukkan abin da suka fada a cikin hukuncin nasu ya zama gaskiya,” in ji Timothy.
Ya ce a maimakon ayyana jam’iyya gaba dayanta a matsayin kungiyar ta’addanci, kamata ya yi kotun ta fadi sunan masu alaka da ta’addancin kai tsaye, musamman a cikin jam’aiyyar APC.
Ya kuma bayyana hukuncin a matsayin na yanke kauna da salon shugabancin gwamnatin Najeriya a karkashin Shugaba Bola Tinubu, inda ya bukaci gwamnatin da kada ta dauki lamarin da wasa.
Sai dai duk kokarinmu na jin ta bakin jam’iyyar APC da gwamnatin tarayya ya ci tura ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.
Masu magana da yawun APC na kasa, Felix Morka da Bala Ibrahim ba su amsa kira rubutaccen sakon da wakilinmu ya tura musu ba, yayin da kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, shi ma bai amsa sakon da wakilinmu ya tura masa ba.
To said ai wani jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa gwamnatin za ta fitar da sanarwa a kan hukuncin a hukumance da zarar ta tabbatar da sahihancin hukuncin.