HausaTv:
2025-05-17@03:43:29 GMT

Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa

Published: 16th, May 2025 GMT

Da safiyar yau Juma’a ne dai jami’an tsaron kasar Chadi su ka kai wani farmaki na   kama tsohon fira minista kuma jagoran ‘yan hamayyar siyasar kasar Succès Masra.

Jam’iyyar hamayya da Masra yake jagoranta, ta bayyana abinda jami’an tsaron su ka yi wa jagoran nata da cewa, garkuwa ce.

 Ita kuwa hukumar kasar ba ta fitar da wani bayani akan kamun Masra ba,wanda shi ne ya zo na uku a zaben shugaban kasar da aka gudanar a shekarar da ta gabata.

A yayin wancan zaben dai shugaban ‘yan hamayyar siyasar ya  riya cewa shi ne wanda ya lashe zaben,amma kuma daga baya ya amince da sakamakon da hukumar zabe ta sanar duk da cewa yana cike da kura-kurai kamar yadda ya bayyana.

Bayanin da jam’iyyar adawar ta masu; Sauyi” ta wallafa a shafinta na ‘facebook’ ya kunshi cewa; shugaba Succes Masra an yi garkuwa da shi da karfin bindiga da safiyar yau 16 ga watan Mayu da misalign karfe; 05; 56 daga gidansa da yake kusa da babbar cibiyar jam’iyyar.

A karkashin sanarwar, Shafin jam’iyyar na ‘facebook’ an kuma wallafa hoton bidiyo na shugaban jam’iyyar yana fitowa daga gidansa zagaye da masu dauke da makamai da suke sanye da kakin soja.

Babban mai shigar da kara na kasar ta Chadi Umar Muhammad Kidilayi ya fada wa kamfanin dillancin labarun Faransa cewa lallai an kama Masra.

Masra dan shekaru 41 ya rike mukamin Fira ministan kasar na tsawon watanni 5 gabanin zaben shugaban kasar da aka yi a watan Mayu na 2024.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

Ƴan majalisar tarayya guda biyu daga jihar Kano, Kabiru Usman da Abdullahi Sani, sun sanar da barin jam’iyyar NNPP zuwa APC a yayin zaman majalisar ranar Alhamis, suna mai nuni da rikice-rikicen cikin gida na jam’iyyar.

Shugaban majalisar Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙun ficewarsu a zaman majalisar, inda ya bayyana cewa Usman na wakiltar mazabar Rano/Bunkure/Kibiya, yayin da Sani na wakiltar Karaye/Rogo.

Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC Gwamna Yusuf Ya Yi Barazanar Ƙwace Lasisin Jerin Gidajen Kwankwasiyya, Amana Da Bandirawo 

Ko da a kwanan baya ma Sanata AbdulRahman Kawu Sumaila da wasu  sun fice daga jam’iyyar NNPP, su ma dai sun ce rikicin ne ya fitar da shi.

Shugaban jam’iyyar APC Abdullahi Ganduje da wasu manyan ƙososhin jam’iyyar sun halarci taron sauyin sheƙar a majalisar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Fira Ministan Spain: Ba Za Mu Yi Mu’amala Da Isra’ila  Mai Kisan Kiyash
  • Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya
  • A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
  • Minista Ya Ƙaryata Ji-ta-ji-tar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London
  • HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
  • NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
  • Kasar Katar Za Ta Sayi Jirage Samfurin Boeing 106 Daga Amurka Da Kudi Dala Biliyan 400
  • Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi
  • Donal Trump Ya Ce Zai Dagewa Kasar Siriya Dukkan Takunkuman Tattalinn Arzikin Da Ta Dora Mata