Dangane da sake fasalin dokar zabe, shugaban hukumar INEC, ya ce hukumar na yin cudanya da majalisar dokokin kasar, inda ya ce makwanni biyu da suka gabata, ta yi wani taro a Legas tare da kwamitin hadin gwiwa na majalisar dattawa da na wakilai kan sake fasalin zabe.

“Majalisar dokoki ta kasa za ta shirya taron jin bahasin jama’a, bayan nan za a samar da kudirin doka, a karshen zancen za a mika wa shugaban kasa domin sanya hannu,” ya

shaida.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki

Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta dakatar da Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano, Muhammad Nazir Yau, na tsawon wata uku domin gudanar da bincike kan zargin yin amfani da kujerarsa ba bisa ƙa’ida ba.

Kansilolinsa sun zarge shi da karkatar da kayayyaki da kuma almundahana wajen tafiyar da dukiyar jama’a.

Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno Lafiyar Tinubu kalau – Soludo

An yanke wannan hukunci ne bayan majalisar ta karɓi rahoto daga kwamitin karɓar koke-koke na jama’a, wanda shugaban marasa rinjaye na majalisar, Hussaini Lawan Cediyar Yangurasa, ya jagoranta a zaman ranar Laraba.

Majalisar ta kuma umarci ma’aikatar ƙananan hukumomi da harkokin masarautu ta jihar da ta bai wa mataimakin shugaban ƙaramar hukumar damar riƙon muƙamin shugaban har sai an kammala bincike.

A cewar rahoton, an zargi Yau da haifar da rigima tsakanin shugabannin siyasa da kansiloli, bayar da kayayyakin gwamnati ga magoya bayansa, rabon takardun shiga makarantar Dangote da takin zamani ba tare da adalci ba.

Hakazalika, an zarge shi da sayar da takin gwamnati sama da farashin da aka amince da shi na Naira 20,000 ba tare da sanar da kansiloli ba.

Har ila yau akwai zarge-zarge da suka haɗa da rashin gaskiya wajen tafiyar da kuɗaɗen shiga daga kasuwanni da kuɗaɗen harajin dabbobi, sayar da rumfunan kasuwa ba tare da izini ba.

Sauran zarge-zargen sun haɗa da raina dattawan jam’iyya da sauran masu ruwa da tsaki, da kuma yin amfani da kuɗaɗen ƙaramar hukuma ba bisa ƙa’ida ba.

Kwamitin ya zauna da ɓangarorin biyu a ranar 11 ga watan Agusta, inda shugaban ya musanta wasu daga cikin zarge-zargen amma ya amince cewa ya ƙara Naira Naira 2,000 a kan farashin takin zamani da gwamnati ta amince da shi.

Bisa ga sashe na 55 na dokar ƙananan hukumomi ta shekarar 2006, kwamitin ya tabbatar da dakatar da shi domin gudanar da cikakken bincike.

Sannan ta umarci a miƙa dukkanin takardun kuɗi da na gudanarwa na ƙaramar hukumar cikin kwanaki bakwai.

A zaman majalisar na ranar Laraba, wanda kakakin majalisar Ismail Falgore ya jagoranta, majalisar ta amince da shawarwarin kwamitin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
  • Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
  • An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su