Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani
Published: 16th, May 2025 GMT
Jami’ar Jihar Kaduna (KASU) ta shiga rudani a ranar Alhamis bayan da aka samu rahotanni masu karo da juna game da matsayin yajin aikin da reshenta na Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ke yi.
Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdullahi Ibrahim Musa, ya gudanar da taron manema labarai inda ya sanar da cewa ASUU-KASU ta dakatar da yajin aikin nata, kuma za a ci gaba da karatun nan take.
Ya danganta matakin janye yajin aikin da shiga tsakani da Gwamna Uba Sani ya yi, wanda ya amince da biyan Naira miliyan 50 miliyan don walwalar ma’aikata, tare da fitar da N146 miliyan don biyan wasu albashin da aka rike da kuma alawus-alawus na shirin koyon makamar aiki na dalibai (SIWES).
Farfesa Musa ya yaba wa wadannan matakan a matsayin “jaruntaka da ba a taba gani ba,” kuma ya jinjinawa gwamnan saboda “halinsa na ban mamaki game da halin da dalibai ke ciki, yanayin ilimi, da walwalar ma’aikatan ilimi da wadanda ba na ilimi ba.”
Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin SambisaYa kuma bayyana cewa an kafa kwamitin sasantawa karkashin jagorancin Mataimakiyar Gwamna Dokta Hadiza Balarabe, don tattaunawa da dukkan kungiyoyin jami’ar domin warware matsalolin da suka dade suna ci mata tuwo a kwarya.
Sai dai jim kadan kuma, ckin kakkausan harshe, ASUU-KASU ta musanta sanarwar Shugaban Jami’ar, inda ta bayyana ta a matsayin katsalandan kuma kuma mara izini.
A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Shugaban kungiyar Kwamared Abubakar Abdullahi da Sakatare Kwamared Peter M. Waziri suka sanya wa hannu, kungiyar ta shawarci jama’a da su yi watsi da ikirarin da hukumar gudanarwar jami’ar ta yi.
Kungiyar ta bayyana cewa, “Ba hukumar gudanarwar Jami’ar ce ta kaddamar da yajin aikin ba, don haka ba ta da ikon dakatar da shi.”
Kungiyar ta nanata cewa har yanzu tana jiran shawarar Majalisar Zartarwarta ta Kasa (NEC) bayan taron majalisar da aka gudanar a ranar 15 ga Mayu, 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yajin aiki yajin aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
A wata hira tare da gidan talabijin na Arise, Obi ya ce duk da cewa cire tallafin mai yana da muhimmanci, amma ya kamata a aiwatar da wannan tsari cikin tsari.
Ya ce ya amince cewa tallafin mai yana cike da ta’asa da cin hanci wanda akwai bukatar a kawo karshensa, amma ya yi suka ga hanyoyin da gwamnatin Tinubu take bi, yana bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa kwarewa ba.
Obi ya tambayi jagororin kula da kudin da aka ajiye daga cire tallafin, yana cewa, “Tun da aka ce manatallafin man fetur, ana cewa an cire ne saboda ba a so mu dunga ciyo bashi kuma kudaden za su ba da dama wajen zuba jari a muhimman ababen more rayuwa.
‘’Ina biliyoyin kudaden da aka tara? Ina aka zuba su a muhimman yankunan ci gaba? Kowa na sane da muhimman yankunan ci gaba da suka hada da ilimi, lafiya, da fitar da mutane daga talauci. Shin ko daya daga cikin wadannan abubuwan gda uku ya inganta? A’a.’’
Obi ya ce ya kamata a yi musayar farashi mai da masu ruwa da tsaki da kyau ta yadda zai rage tasirin ga matsalolin da ‘yan kasa ke ciki.
Da yake mayar da martini ga Obi, mai taimaka wa shugaban kasa kan batutuwan tsare-tsare, Daniel Bwala, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a matsayin mutum mai son kansa wanda ba ya da ilimin warware al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci.
Bwala, a cikin wata sanarwa da ya wallafa ta shafinsa na sada zumunta na Tuwita, ya bayyana cewa ya yi mamakin yadda Obi ya yarda da manufofin tattalin arzikin Shugaba Tinubu, musamman kan cire tallafin mai da hada-hadar kudaden waje, amma ya jaddada cewa Obi sauran manyan ‘yan adawa suna neman samun iko ne kawai ko ta wani hali a wannan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp