Aminiya:
2025-06-14@14:02:31 GMT

Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba 

Published: 16th, May 2025 GMT

Sojojin da suke aiki a ƙarƙashin rundunar birget ta 6 da ke garin Jalingo a Jihar Taraba sun kashe ’yan bindiga biyu tare da ƙwato shanu guda dubu ɗaya daga hannun ɓarayin shanu.

Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na rundunar sojoji ta birget ta 6 da ke garin Jalingo, Kyaftin Oni Olubodunde ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a garin Jalingo a ranar Juma’a.

Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno

Ya ce, nasarar ƙwato shanu tare da kashe ’yan bindigar ya kasance ne biyo bayan wani bayanan sirri da rundunar ta samu dangane da shuguban wasu guggun ’yan bindigar akan bubura talatin inda suka shiga wani yanki na Ƙaramar hukumar Karim Lamiɗo domin satar shanun makiyaya.

Kyaftin Oni ya bayyana cewa, yan ta’addan sun shigo Jihar Taraba ne daga Jihar Filato domin aikata ta’addanci tare da sace shanu.

Ya ƙara da cewa, ’yan ta’addan sun shiga yankin Jebjeb ne domin satar shanu a wasu rugagen Fulani, amma dubunsu ta cika inda sojojin suka kashe biyu daga cikinsu kuma suka fatattaki sauran tare ƙwato shanu har dubu ɗaya waɗanda su ’yan ta’addan suka sace.

Ya ce, a halin yanzu sojojin na tantace masu shanu domin a mayar masu da shanun su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karim Lamido Taraba ƙwato shanu

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas

A cewarsa, gobarar na iya kasancewa ta samo asali ne daga wani gini da ke bayan gidan man.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar na iya tashi ne daga tankunan mai da ke ƙasa, kafin ta bazu zuwa cikin gidan man gaba ɗaya.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta yi gaggawar killace wajen domin hana cunkoso da tabbatar da tsaron jama’a yayin aikin kashe gobarar.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobarar, Shakiru Amodu, ya tabbatar da cewa an samu nasarar kashe gobarar kafin ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.

Kafin ƙarfe 6 na yamma, jami’an agajin gaggawa sun shawo kan lamarin gaba ɗaya, tare da killace yankin da abin ya shafa domin kaucewa wata barazana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato
  • Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya