Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba
Published: 16th, May 2025 GMT
Sojojin da suke aiki a ƙarƙashin rundunar birget ta 6 da ke garin Jalingo a Jihar Taraba sun kashe ’yan bindiga biyu tare da ƙwato shanu guda dubu ɗaya daga hannun ɓarayin shanu.
Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na rundunar sojoji ta birget ta 6 da ke garin Jalingo, Kyaftin Oni Olubodunde ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a garin Jalingo a ranar Juma’a.
Ya ce, nasarar ƙwato shanu tare da kashe ’yan bindigar ya kasance ne biyo bayan wani bayanan sirri da rundunar ta samu dangane da shuguban wasu guggun ’yan bindigar akan bubura talatin inda suka shiga wani yanki na Ƙaramar hukumar Karim Lamiɗo domin satar shanun makiyaya.
Kyaftin Oni ya bayyana cewa, yan ta’addan sun shigo Jihar Taraba ne daga Jihar Filato domin aikata ta’addanci tare da sace shanu.
Ya ƙara da cewa, ’yan ta’addan sun shiga yankin Jebjeb ne domin satar shanu a wasu rugagen Fulani, amma dubunsu ta cika inda sojojin suka kashe biyu daga cikinsu kuma suka fatattaki sauran tare ƙwato shanu har dubu ɗaya waɗanda su ’yan ta’addan suka sace.
Ya ce, a halin yanzu sojojin na tantace masu shanu domin a mayar masu da shanun su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Karim Lamido Taraba ƙwato shanu
এছাড়াও পড়ুন:
An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
Hukumar kula da makarantun firamare da sakandare ta Jihar Katsina ta sanar da sake buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarabawar zangon farko na shekarar karatu.
A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sani Danjuma Suleman, ya fitar a madadin Shugaban hukumar, ta ce makarantun firamare, sakandiren je-ka-ka-dawo da kuma makarantu masu zaman kansu za su buɗe daga yau Talata domin ci gaba da jarabawar zangon farko.
Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran makarantun kwana za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai lokacin da hali ya ba da dama.
Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamnatin Katsina ta rufe makarantun bayan ƙaruwar hare-haren sace ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka sake farfaɗowa da su a wasu yankuna.
Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne da nufin daƙile matsalar tsaro da kuma sa ido a kan al’amura.
A ƙarshe, hukumar ta roƙi haɗin kan iyaye da masu kula da ɗalibai domin su ci gaba da ba wa shirin goyon baya tare da ƙarfafa ɗaliban su dage da karatu wajen rubuta jarabawar da suke yi.