Aminiya:
2025-05-17@03:45:49 GMT

Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba 

Published: 16th, May 2025 GMT

Sojojin da suke aiki a ƙarƙashin rundunar birget ta 6 da ke garin Jalingo a Jihar Taraba sun kashe ’yan bindiga biyu tare da ƙwato shanu guda dubu ɗaya daga hannun ɓarayin shanu.

Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na rundunar sojoji ta birget ta 6 da ke garin Jalingo, Kyaftin Oni Olubodunde ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a garin Jalingo a ranar Juma’a.

Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a Borno

Ya ce, nasarar ƙwato shanu tare da kashe ’yan bindigar ya kasance ne biyo bayan wani bayanan sirri da rundunar ta samu dangane da shuguban wasu guggun ’yan bindigar akan bubura talatin inda suka shiga wani yanki na Ƙaramar hukumar Karim Lamiɗo domin satar shanun makiyaya.

Kyaftin Oni ya bayyana cewa, yan ta’addan sun shigo Jihar Taraba ne daga Jihar Filato domin aikata ta’addanci tare da sace shanu.

Ya ƙara da cewa, ’yan ta’addan sun shiga yankin Jebjeb ne domin satar shanu a wasu rugagen Fulani, amma dubunsu ta cika inda sojojin suka kashe biyu daga cikinsu kuma suka fatattaki sauran tare ƙwato shanu har dubu ɗaya waɗanda su ’yan ta’addan suka sace.

Ya ce, a halin yanzu sojojin na tantace masu shanu domin a mayar masu da shanun su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karim Lamido Taraba ƙwato shanu

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa sabuwar rundunar masu tsaron daji a faɗin ƙasar nan domin tinkarar matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a cikin dazukan Najeriya.

A ƙarƙashin wannan sabon shiri, za a ɗauki sama da mutane 130,000 aiki da za su samu horo na musamman da kayan yaƙi na zamani domin kare dazuka guda 1,129 da ke sassa daban-daban na ƙasar nan.

Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe

Wannan na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Sunday Dare, ya fitar a shafinsa na X.

Sanarwar ta bayyana cewa an amince da shirin ne a lokacin taron majalisar zartarwa ta tarayya da aka gudanar ranar Litinin.

A cewar sanarwar, shugaba Tinubu, ya umarci kowace jiha da ta ɗauki ma’aikata daga 2,000 zuwa 5,000 bisa ƙarfin kasafin kuɗinta, domin zama ’yan tsaron daji.

Ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro da ma’aikatar muhalli za su sanya ido a kan tsarin ɗaukar ma’aikatan da horar da su.

Babban aikin waɗannan masu tsaron dajin shi ne fatattakar ’yan ta’adda da miyagu da ke ɓuya a dazuka suna aikata laifuka.

Sanarwar ta ƙara da cewa Shugaba Tinubu ya bayyana buƙatar a bai wa masu aikin horo mai kyau da makamai na zamani domin kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
  • Sabon Hari: An kashe makiyaya 1 da shanu sama da 100 a Filato
  • Yadda ’yan bindiga suka kashe jarirai, suka bai wa karnuka namansu a Zamfara 
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi