Leadership News Hausa:
2025-05-16@15:56:38 GMT

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Published: 16th, May 2025 GMT

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Haramun ne ga mai harama namiji ya daura duk wani abu dinkakke, sai dai hirami kawai. Amma idan bai samu hirami ba, babu laifi ya daura wando kamar yadda Abdullahi bin Abbas (RA) ya ruwaito daga cikin hudubar da Annabi (SAW) ya yi a ranar Arfa.

Idan mai harama bai samu silafas ba, zai iya sanya takalmi sawu-ciki, amma ya yanke shi zuwa karkashin idon sawunsa kamar yadda ake wa khuffi.

Wannan duk an haramta ne ga namiji. Amma ita mace babu abin da ya haramta mata illa sanya turare, nikabi da safar hannu, kamar yadda Abdullahi bin Umar (RA) ya ruwaito daga Manzon Allah (SAW). Haka nan kar ta sanya kayan da aka yi musu rini da turare, amma idan rini ne kawai babu turare shikenan. Bayan wannan, za ta iya sanya duk abin da take so.

Akwai Malaman da suka yi shisshigin cewa mace za ta iya sanya nikabi, amma kuma ya kamata a fahimci cewa idan Shari’a ta zo da abu, namu bi ne kawai. Don wandanda suke ganin za a iya rufe fuskar saboda kishin matan ai ba su kai Annabi (SAW) kishi ba. Ya kamata a yi hattara.

Haramun ne mai harama da Hajji ya yi aure ko ya daura wa wani ko wakilta wani. Idan kuma aka yi, to ya baci.

Ba a yarda mai harama ya yanke farce ko cire gashinsa a ko wace gaba ba (askewa ko ragewa). Amma an yi sauki idan farcen ya karye, babu laifi a cire gutsiren da ya rage shi kadai. Idan kuma yana cutuwa da gashin wani wuri a jikinsa, zai iya cirewa amma sai ya ba da hadaya.

Game da gashin gira, sauran Maz’habobi sun ce za a iya cirewa babu komai, amma Imam Malik ya ce shi ma sai an ba da hadaya.

Haramun ne sanya turare walau ga namiji ko mace. Za a iya sanyawa ne kafin a yi harama. Hatta Alhajin da ya mutu a wurin Aikin Hajji ba a sanya ma sa turare bayan an ma sa wanka. Annabi (SAW) ya ce “Idan Alhaji ya mutu, kar a rufe ma sa kai, kar a sanya ma sa turare, zai tashi ranar kiyama a matsayin Alhaji.”

Babu laifi idan turaren da ake shafa wa Ka’aba ya shafi mayafin Alhaji, ba sai ya wanke ba. Amma dai kar mutum ya je da gangar da nufin shafawa.

Haramun ne ga mai harama ya yi farauta a kan kasa ko ya nuna wa wani abin farautar ko ya taimaka wa mai yi, amma ya halasta ya yi a cikin ruwa kuma ya ci. Hukuncin wanda ya aikata daya daga cikin abubuwan nan da aka hana bisa uzuri (ban da saduwa da iyali) shi ne, ya ba da hadayar akuya. Idan ba shi da ita sai ya ciyar da miskinai shida. Ko wane miskini a bashi rabin sa’i. Ko kuma ya yi azumin kwana uku. Wanda ya yanke gashinsa guda uku ko abin da ya fi haka, zai yi fidiya da akuya. Imamus Shafi’i ya ruwaito cewa idan mutum ya tsige gashi daya, hukuncinsa shi ne ya ba da abinci cikin tafi daya (Muddan Nabiy daya), idan ya tsige biyu; zai ba da biyu, idan yawansu ya kai uku; sai ya ba da jini (akuya).

Haka nan ba a so Alhaji ya shafa mai (mai kamshi ko mara kamshi) lokacin da yake cikin harami. Idan ya shafa, hukuncin ba da jini (akuya) ya hau kansa. Imam Abu Hanifa ya ce a ko wace gaba aka shafa; wannan hukuncin ya hau kan mutum, ba a kebe wasu gabobi da aka amince a shafa musu ba. Amma a wurin Imam Shafi’i, idan an shafa wa kai ko gemu ne hukuncin jinin yake aukuwa. Koda yake shi ya yi sauki a kan shafa mai mara kamshi, sai dai shi ma ban da kai da gemu.

 

Hukuncin Saduwa Da Iyali A Hajji

Babu abin da yake bata Aikin Hajji kada’an da ba za a iya gyarawa da kaffara ba sai Saduwa da iyali.

Sayyidina Aliyu (RA) da Sayyidina Umar (RA) da Sayyidina Abu Huraira (RA) sun ba da fatawar cewa duk wanda ya sadu da iyalinsa bayan ya yi harama da Aikin Hajji, Hajjinsa ya baci. Kuma wajibi ne ya ci gaba da aikin har ya kammala. Sannan zai ba da rakumi ko saniya, ya kuma dawo wata shekarar ya sake yin wani Hajjin.

Abul Abbasid Dabari, ya ce idan mai Aikin Hajji ya sadu da iyalinsa kafin halastawa karama, Hajjinsa ya baci. Ma’anar halastawa karama ita ce daga lokacin da mutum ya yi harama zuwa tsayuwar Arfa har zuwa Jifa na ranar Sallah da hadaya da aski ko saisaye, sai bai samu ya tafi Makka ya yi Dawafi ba, to an halasta ma sa abubuwan da aka haramta ma sa lokacin da ya yi harama (irin su sanya kayan gida, aski, shafa turare, shafa mai da sauran su) amma ban da saduwa da iyali.

Ita ma matar da aka sadu da ita alhali ta yi harama da Hajji, Hajjin nata ya lalace, kamar yadda wasu malamai suka bayyana. Ita ma za ta karasa sauran ayyukan da suka rage, kuma za ta ba da jini (rakumi ko saniya). Koda yake akwai Malaman da suka ce idan ita da mijin suka ba da daya (rakumin ko saniya) ya isar musu, ba sai ita matar ta bayar da nata daban ba.

Idan za su dawo wata shekarar su rama Hajjin, shari’a ta ce a raba tsakaninsu domin rigakafin sake aukuwar hakan.

Idan wanda ya sadu da iyalinsa ya kasa ba da rakumi; sai ya ba da saniya, idan ya kasa; sai ya ba da awaki, idan ya kasa; sai a yi ma sa kimar kudin rakumin ko lissafin adadin abinci ya bayar. Ko wane Miskini zai ba shi Muddan Nabiy daya. Idan kuma bai samu ba, sai ya yi azumi na adadin yawan Muddan Nabiy da zai bayar.

Amma su a wurin Ma’abota Zahiri, idan mutum ya sadu da iyalinsa Hajjinsa ya baci sai dai zai ba da akuya ne kawai.

A wani hukuncin kuma, idan mutum ya sadu da iyalinsa bayan halastawa karama, to babu komai a kansa, kamar yadda galibin Malamai suka tafi a kai. Sai dai wani sashen na Malamai sun ce mutum zai rama kuma hadaya ta wajaba a kansa, kamar yadda aka ruwaito daga Abdullahi bin Umar (RA), Hasanul Basri, Ibrahimun Naka’i. Abdullahi bin Abbas (RA) ya karfafa batun ba da rakumi kamar yadda shi ma Ikrimah ya fada. Imamu Malik da Imamu Shafi’i su kuma sun yi sauki inda suka ce a ba da akuya.

Idan Alhaji ya yi mafarki ya sadu da iyalinsa har maniyyi ya fito, ko ya dinga tunanin saduwa har maziyyi ya fito ma sa ko kuma saboda kallo na sha’awa ya fitar, Hajjinsa bai baci ba kuma babu komai a kansa. Saboda yin hakan ba saduwa ba ce. Amma kuma duk wanda ya shafa mace da nufin sha’awa ko ya sumbace ta da sha’awa; zai ba da akuya, walau ya fitar da maniyyi ko maziyyi ko bai fitar ba. An ruwaito wannan ma daga Abdullahi bin Abbas (RA).

Yana da matukar kyau kowa ya kiyaye wadannan abubuwa domin a samu Hajjin da ya kubuta daga dukkan aibi, ma’ana Hajjan Mabrur.‎ Allah ya ba da iko.

Idan Allah ya kai mu mako mai zuwa, in sha Allahu za mu zo da bayani a kan abubuwan da ake so mai shiga Makka ya aikata. Allah ya nuna mana cikin koshin lafiya.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Umrah ya sadu da iyalinsa sai ya ba da a yi harama kamar yadda

এছাড়াও পড়ুন:

Sabon Hari: An kashe makiyaya 1 da shanu sama da 100 a Filato

A wasu rahotanni sun ce an kashe makiyayi guda ɗaya da shanu sama da 100 a wasu hare-hare da aka kai hari kan makiyaya a wasu ƙauyuka biyu da ke ƙananan hukumomin Jos ta Kudu da Jos ta Arewa a Jihar Filato.

Hare-haren da ake zargin wasu ’yan bindiga ne da suka buɗe wa makiyaya wuta a lokacin da suke kiwo, wanda ke nuna rashin tsaro a yankunan da aka daɗe ana fama da rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya, lamarin da ke janyo asarar rayuka.

Dalilin da ya sa gwamna Bala ya yi ƙoƙarin mari na – In ji Minista Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa

Sakataren Ƙungiyar Miyetti Allah Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) na jihar Ibrahim Yusuf Babayo ya tabbatar da faruwar lamarin tare da zargin ’yan ƙabilar rukunin Berom daga na da hannu wajen kai harin.

Sai dai shugabannin Ƙungiyar matasan Berom sun musanta zargin da ake yi musu, inda suka yi watsi da hakan a matsayin farfaganda.

Daily Trust ta samu rahoton cewa, harin farko ya faru ne da yammacin ranar Talata a unguwar Gero da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Kudu, yayin da na biyu kuma ya faru ne da safiyar Laraba a unguwar Darwat da ke Ƙaramar hukumar Riyom.

A cewar Babayo, makiyaya uku sun samu raunuka a harin na Gero. A halin yanzu ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa na yin jinya a wani Asibiti da ke Jos, yayin da sauran biyun kuma ke jinya a Asibitin Sojoji da ke barikin Rukuba a Jos.

“A ranar 13 ga Mayu, 2025, matasan Berom daga Gero, Gundumar Ngel a Jos ta Kudu, sun haɗa baki suka farwa makiyayan shanu, inda suka kashe shanu kusan 70.

“Sun yanka wasu daga cikin shanun tare da sace naman, sojojin hedikwatar Operation Safe Haɓen sun shiga tsakani suka kama wasu mutane uku da aka samu da naman shanun da aka yanka,” in ji Babayo.

Ya ci gaba da cewa, “A ranar 14 ga Mayu, 2025, matasan Berom a Darwat sun zo da yawa, suka fara harbin shanu na mambobinmu.

“Sun kashe shanu sama da 40, sun yanka wasu, suka kwashe naman, ba tare da wata tsokana ba, haka kawai suka fara harbe-harbe a kan dabbobin, harin da ake zargin an shirya ne, ba mu da wata kariya, na sanar da hukumar rundunar GOC 3 da kuma daraktan tsaro na jihar halin da ake ciki.”

Babayo ya kuma bayyana cewa waɗannan hare-haren wani ɓangare ne na tada hankali.

Ya ƙara da cewa, “A cikin makonni biyun da suka gabata, an samu irin wannan harin inda aka kai wa makiyaya da shanunsu hari, waɗannan hare-haren sun yi sanadin asarar rayukan mutane da kuma satar dabbobi, a ranar Litinin kaɗai, an ce an samu ɓacewar wani makiyayi, an kuma yi awon gaba da shanu 41 a Bisichi.”

“A kullum ana kashe mu, da alama ana tsokanar mu, muna kira ga gwamnati da ƙasashen duniya da su lura da abin da ke faruwa a Jihar Filato, a matsayinmu na ’yan ƙasa masu bin doka, muna kira ga mambobinmu da su kwantar da hankalinsu, muna kuma kira ga hukumomin tsaro da su kawo ƙarshen wannan kashe-kashe na rashin hankali da kuma kare Fulani makiyaya daga ci gaba da kai hari,” in ji Babayo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • GORON JUMA’A 16/05/2025
  • BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa
  • Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS
  • Sabon Hari: An kashe makiyaya 1 da shanu sama da 100 a Filato
  • Rasha Ta Ce Putin Ba Zai Halarci Tattaunawar Zaman Lafiya A Istanbul Ba
  • Najeriya ba za ta koma mulkin soja ba — Gowon
  • ’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a Zamfara 
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci Gwamnati Ta Kai Dauki Ga Wadanda Iftila’in Guguwa Ya Shafa
  • Mali : An rushe dukkan jam’iyyun siyasa a hukumance