Leadership News Hausa:
2025-08-15@04:43:57 GMT

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Published: 16th, May 2025 GMT

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Haramun ne ga mai harama namiji ya daura duk wani abu dinkakke, sai dai hirami kawai. Amma idan bai samu hirami ba, babu laifi ya daura wando kamar yadda Abdullahi bin Abbas (RA) ya ruwaito daga cikin hudubar da Annabi (SAW) ya yi a ranar Arfa.

Idan mai harama bai samu silafas ba, zai iya sanya takalmi sawu-ciki, amma ya yanke shi zuwa karkashin idon sawunsa kamar yadda ake wa khuffi.

Wannan duk an haramta ne ga namiji. Amma ita mace babu abin da ya haramta mata illa sanya turare, nikabi da safar hannu, kamar yadda Abdullahi bin Umar (RA) ya ruwaito daga Manzon Allah (SAW). Haka nan kar ta sanya kayan da aka yi musu rini da turare, amma idan rini ne kawai babu turare shikenan. Bayan wannan, za ta iya sanya duk abin da take so.

Akwai Malaman da suka yi shisshigin cewa mace za ta iya sanya nikabi, amma kuma ya kamata a fahimci cewa idan Shari’a ta zo da abu, namu bi ne kawai. Don wandanda suke ganin za a iya rufe fuskar saboda kishin matan ai ba su kai Annabi (SAW) kishi ba. Ya kamata a yi hattara.

Haramun ne mai harama da Hajji ya yi aure ko ya daura wa wani ko wakilta wani. Idan kuma aka yi, to ya baci.

Ba a yarda mai harama ya yanke farce ko cire gashinsa a ko wace gaba ba (askewa ko ragewa). Amma an yi sauki idan farcen ya karye, babu laifi a cire gutsiren da ya rage shi kadai. Idan kuma yana cutuwa da gashin wani wuri a jikinsa, zai iya cirewa amma sai ya ba da hadaya.

Game da gashin gira, sauran Maz’habobi sun ce za a iya cirewa babu komai, amma Imam Malik ya ce shi ma sai an ba da hadaya.

Haramun ne sanya turare walau ga namiji ko mace. Za a iya sanyawa ne kafin a yi harama. Hatta Alhajin da ya mutu a wurin Aikin Hajji ba a sanya ma sa turare bayan an ma sa wanka. Annabi (SAW) ya ce “Idan Alhaji ya mutu, kar a rufe ma sa kai, kar a sanya ma sa turare, zai tashi ranar kiyama a matsayin Alhaji.”

Babu laifi idan turaren da ake shafa wa Ka’aba ya shafi mayafin Alhaji, ba sai ya wanke ba. Amma dai kar mutum ya je da gangar da nufin shafawa.

Haramun ne ga mai harama ya yi farauta a kan kasa ko ya nuna wa wani abin farautar ko ya taimaka wa mai yi, amma ya halasta ya yi a cikin ruwa kuma ya ci. Hukuncin wanda ya aikata daya daga cikin abubuwan nan da aka hana bisa uzuri (ban da saduwa da iyali) shi ne, ya ba da hadayar akuya. Idan ba shi da ita sai ya ciyar da miskinai shida. Ko wane miskini a bashi rabin sa’i. Ko kuma ya yi azumin kwana uku. Wanda ya yanke gashinsa guda uku ko abin da ya fi haka, zai yi fidiya da akuya. Imamus Shafi’i ya ruwaito cewa idan mutum ya tsige gashi daya, hukuncinsa shi ne ya ba da abinci cikin tafi daya (Muddan Nabiy daya), idan ya tsige biyu; zai ba da biyu, idan yawansu ya kai uku; sai ya ba da jini (akuya).

Haka nan ba a so Alhaji ya shafa mai (mai kamshi ko mara kamshi) lokacin da yake cikin harami. Idan ya shafa, hukuncin ba da jini (akuya) ya hau kansa. Imam Abu Hanifa ya ce a ko wace gaba aka shafa; wannan hukuncin ya hau kan mutum, ba a kebe wasu gabobi da aka amince a shafa musu ba. Amma a wurin Imam Shafi’i, idan an shafa wa kai ko gemu ne hukuncin jinin yake aukuwa. Koda yake shi ya yi sauki a kan shafa mai mara kamshi, sai dai shi ma ban da kai da gemu.

 

Hukuncin Saduwa Da Iyali A Hajji

Babu abin da yake bata Aikin Hajji kada’an da ba za a iya gyarawa da kaffara ba sai Saduwa da iyali.

Sayyidina Aliyu (RA) da Sayyidina Umar (RA) da Sayyidina Abu Huraira (RA) sun ba da fatawar cewa duk wanda ya sadu da iyalinsa bayan ya yi harama da Aikin Hajji, Hajjinsa ya baci. Kuma wajibi ne ya ci gaba da aikin har ya kammala. Sannan zai ba da rakumi ko saniya, ya kuma dawo wata shekarar ya sake yin wani Hajjin.

Abul Abbasid Dabari, ya ce idan mai Aikin Hajji ya sadu da iyalinsa kafin halastawa karama, Hajjinsa ya baci. Ma’anar halastawa karama ita ce daga lokacin da mutum ya yi harama zuwa tsayuwar Arfa har zuwa Jifa na ranar Sallah da hadaya da aski ko saisaye, sai bai samu ya tafi Makka ya yi Dawafi ba, to an halasta ma sa abubuwan da aka haramta ma sa lokacin da ya yi harama (irin su sanya kayan gida, aski, shafa turare, shafa mai da sauran su) amma ban da saduwa da iyali.

Ita ma matar da aka sadu da ita alhali ta yi harama da Hajji, Hajjin nata ya lalace, kamar yadda wasu malamai suka bayyana. Ita ma za ta karasa sauran ayyukan da suka rage, kuma za ta ba da jini (rakumi ko saniya). Koda yake akwai Malaman da suka ce idan ita da mijin suka ba da daya (rakumin ko saniya) ya isar musu, ba sai ita matar ta bayar da nata daban ba.

Idan za su dawo wata shekarar su rama Hajjin, shari’a ta ce a raba tsakaninsu domin rigakafin sake aukuwar hakan.

Idan wanda ya sadu da iyalinsa ya kasa ba da rakumi; sai ya ba da saniya, idan ya kasa; sai ya ba da awaki, idan ya kasa; sai a yi ma sa kimar kudin rakumin ko lissafin adadin abinci ya bayar. Ko wane Miskini zai ba shi Muddan Nabiy daya. Idan kuma bai samu ba, sai ya yi azumi na adadin yawan Muddan Nabiy da zai bayar.

Amma su a wurin Ma’abota Zahiri, idan mutum ya sadu da iyalinsa Hajjinsa ya baci sai dai zai ba da akuya ne kawai.

A wani hukuncin kuma, idan mutum ya sadu da iyalinsa bayan halastawa karama, to babu komai a kansa, kamar yadda galibin Malamai suka tafi a kai. Sai dai wani sashen na Malamai sun ce mutum zai rama kuma hadaya ta wajaba a kansa, kamar yadda aka ruwaito daga Abdullahi bin Umar (RA), Hasanul Basri, Ibrahimun Naka’i. Abdullahi bin Abbas (RA) ya karfafa batun ba da rakumi kamar yadda shi ma Ikrimah ya fada. Imamu Malik da Imamu Shafi’i su kuma sun yi sauki inda suka ce a ba da akuya.

Idan Alhaji ya yi mafarki ya sadu da iyalinsa har maniyyi ya fito, ko ya dinga tunanin saduwa har maziyyi ya fito ma sa ko kuma saboda kallo na sha’awa ya fitar, Hajjinsa bai baci ba kuma babu komai a kansa. Saboda yin hakan ba saduwa ba ce. Amma kuma duk wanda ya shafa mace da nufin sha’awa ko ya sumbace ta da sha’awa; zai ba da akuya, walau ya fitar da maniyyi ko maziyyi ko bai fitar ba. An ruwaito wannan ma daga Abdullahi bin Abbas (RA).

Yana da matukar kyau kowa ya kiyaye wadannan abubuwa domin a samu Hajjin da ya kubuta daga dukkan aibi, ma’ana Hajjan Mabrur.‎ Allah ya ba da iko.

Idan Allah ya kai mu mako mai zuwa, in sha Allahu za mu zo da bayani a kan abubuwan da ake so mai shiga Makka ya aikata. Allah ya nuna mana cikin koshin lafiya.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Umrah ya sadu da iyalinsa sai ya ba da a yi harama kamar yadda

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128

128-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka  barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafai wadanda suka hada sa littafin Dastane Rastantan ko kuma cikin littafin mathnawi na maulana jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasashence tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan Al-Mutaba, (a) dan Fatima (s) diyar manzon All..(s) da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata. Mun bayyana yadda Imam Ali (a) ya kammala hujja a kan mutanen Jamal bayan bi hanyoyi da daman a hana zubar da jinin musulmi amma suka ki amincewa.

Abu na karshe da yayi shi ne ya fiyar da mushafin alkur’ani ya fara bin sahu-sahu na sojojinsa, yana cewa wa zai karbi wannan alkur’ani ya bijiro masa, ya ce masu wannan ya shiga tsakanim, ina kiranku zuwa ga littafin All..idan an yanke damarsa, ya rike da hannunsa na hagu idan an katse ta da hakoransa, ya ce za’a kasashe shi. Sai wani matashi dan kufa ya ce shi zai yi. Da farko Imam (a) ya yi watsi da shi, amma ba wanda ya amsa kiransa sai wannan matashin sai daga karshe ya bashi, ya kuma bayyana masa abinda zau fada masu.

Wannan matashin. ba tare da tsaron ba ya je ya aiwatarn da umurnin Imam, kamar yadda ya umurceshi, ya kuma kai ga shahada.

Daga nan ya ce jininsu ya halatta da wannan manzonsa na karseh da suka kashe. Don haka ya kira kwamandojin sojojinsa ya kuma bayyana masu dokokin yaki, musamman a yaki tsakanin musulm mi. Ya hanasu, kashe wanda suka ji rauni, kada su bi wanda ya gudu, kada su kashe wanda ya bada baya, kada su dauki ganima sai makamai da abin hawa a yaki. Sauran abinda ya rage na dukiyoyinsu, kamar kuyangu, bayi da sauransu na masu gadonsu ne, kamar yadda alkur’ani ya kawo.

Sannan ya bawa dansa Muhammad ibnul Hanafiyya, tutarsa, a lokacinda aka fara yaki sai ya ga rauni a waje, sai yazo ya karbi tutar a wajensa ya kuma kutsa tsakiyar yakin yana kashewa dama da hagu.

Sannan munji yadda ya hadu da Zubai a tsakiyar yakin ya kuma tunatar da shi hadisin wanzon All..(s) gareshi cewa zai yake shi, sai Zubair ya fita daga cikin yakin, amma ya je wani wuri wajen yakin sai wasu mutane tare da Al-Ahnaf  suka kashe shi yana basu sallah. Wannan shi ne karshen Zubair.

Sanna da alamun an bada umurni a kashe shi daga rundunar Aisha bayan ya fice daga cikinsu.

A yakin Jamal babba dai, kabilu 3 ne suka fi taimakawa runduranr aisha, kabilar Al-Azdi da Banu dhubba, da kuma banu Najiya. Malaman tarihin sun bayyana cewa Banu al-Al-azdi, wadanda suke kewaye da rakuminta suna rare kasidu na yabonta.

An ruwaitota tana yabonsu, suka kuma mutuwa a gabanta. Wannan halin ya ci gaba, ko wane bangare yana son kare shugabansa. An yawaita kisa a tsakanin musulmi.

Daga nan Imam Imam(a) ya ga cewa yakin ba zai kawo karshe ba matukar wannan rakumin na aisha tana tsaye.

Sai ya kira Ammar dan Yasir da kuma Malik alashtar biyu daga cikin kwamnadojinsa, a lokacinda suka zo sai yace masu: ku je ku buke soke wannan rakumin, Lalle yakin ba zai kare ba matukar tana raye, don Lalle sun maida ita Al-kibla..

Daga nan sai suka dauko wasu mayaka suka nufeta, sai wani matashi mai suna  Mu’ammar dan Abdullahi wanda ya buge ta tsakanin guiwa sa cinyanta. Wasu sun ce da farko Imam (a) ya bawa dansa Muhammad dan Hanafiyya kibiya ya habeta, sai yaje ,amma masu gadin Aisha sun hanashi sai ya dawo sannan Imam Hassan ya krbi kibiyar ya je ya kuma sameta a kafarta.

Don haka da aka bugeta a kafa da fada kasa ta yi wani kara wand aba shi da kyau jinsa, kuma ba’a taba jin irin wannan karar ba. Da zaran ta fadi sai wadanda suke kewaye da ita suka tarwatse.  Don gunkin da suka gabatar masa jinni ya fadi.

Daga baya Imam (a) ya bada umurni a konata a kuma watsa tokanta a cikin ruwa ta yadda babu abinda zai rage na jikinta, wanda zai sa wawaye su bauta mata.

Bayan an yi da ita haka, sai yace: All..ya ysinewa wannan dabban, ta yi kamada dan marakin banu isra’ila.

A lokacinda aska ta kada tokanta ya tashi sama sai yace: {Ka yi dubi zuwa ga ubangijinka wanda baka gushe ba kana bautansa  Lallei sai mun kona shi, sannan mu watsa shi cikin kogi watsa wa} Taha 20.

Daga nan sai Imam (a) yayi afwa ga Aisha, ya aika dan uwanta Muhammad dan Abubakar ya je ya fito da ita daga Haudaju, ko rumfan mata a kan rakumi, sai Muhammad ya je ya sa hannusa a cikin haudajun yana neman kama hannunta ya fitar da ita, sai ta janye hannunta, tana cewa, waye wannan

Sai tace: wanda kika fi ki a cikin danginki, sai ta gane shi, tana kyamarsa, sai tace mata ibn Hathamiyya? Sai yace . sai ta juya fuskanta daga gareshi, sai y ace mata akwai abinda ya sameki. Sai tace: wata kibiya amma bata ji mani ciwo ba. Sai ya cireta daga sai ya fito da ita daga Haudajinta, yana tare da ita har ya shigar da ita Basra a cikin dare, a gidann Abdullahi dan Khanaf al-khuzaee. Wajen matarsa Safiyatu yar Haritha. Sai ta zauna yan kwanaki a wajenta.

Imam Ali (a) ya shelanta afwa na gama gari ga dukkan makiyansa, wadanda suka yake shi ko suka yi adawa shi. A cikin wannan halin ne sai Aisha matar manzon All..ta aika wa Imam (a) tana nemawa dan yar’uwanda Abdullahi dai Zubair afwa. Saboda mahaifar Adullahi yayar Aisha  ce, wato  Asmau diyar Abubakar khalif ana farko.

Kamar yadda muka karanta a bayan Abdullahi dan Zubair a yayi khuduba a Basra, yana tuhumar Imam Ali(a) da kashe Uthman a fili, ya kuma bukaci mutanen Basra su dauki fansar jinin Uthman daga Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a). sai Imam Ali (a) yace ya gafarta masa.

Sannan Marwan dan Hakan, ya biyo ta Imam Al-Hassan da Al-Hussain (a) don su nemammasa Afwa daga mahaifinsu Imam Ali (a). shi ma ya amince ya yi masa Fawa. Sanna tun lokacinda aka kawo karshen yakin Imam Ali (a) tura mai shelansa yana shela yana cewa: Ku saurar, kada ku karasa wanda jiwa ciwo, kada a bi Wanya ke ya juya yana gudu, kada a buge wanda ya juya baya yana gudu, duk wanda ya yada takobinsa amintecce ne, wanda ya shiga gidansa ya kulle amintacce ne.  

Sannan Ya’akubi ya kawo a cikin tarihinsa Jz 2 shafi 159, kan cewa aka amintar da baki da ja, sai cutar da mutum ko guda daga cikin wadanda husuma da shi ba. Don haka zai zaman lafiya ya game ko ina bayan yakin. Nutsuwa ta game dukkan yankunan Basra.

Daga nan sai Amirul muminina (a) ya aiki Abdullahi dan Abbas ya je masaukin Aisha matar manzon All..(s) a Basra ya ce mata ta shirya komawa dakinta a Madina, kamar yadda All..ya umurceta. Sai ibnu Abba ya je gidan ya kuma nemi izijin shiga wajenta, sai taki ta bashi ijinin shi wajenta. Sai ibn Abba ya kutsa cikin dakin ba tare da izininta ba, sai ya ga wani batashin kai a dakin sai ya jawo shi ya zauna a kai. Sai ta ji zafi hakan da yayi, sai tace masa. Walla ya kai dan Abbas ban taba ganin irinka ba, ka shiga daki na, ka dauki matashin kai na, ka zauna a kansa  ba tare da amincewarmu ba.!!.

Sai Ibn Abbas yace mata: Na rantse da All..ba dakin ki ba ne, dakin ki kawai shi ne wanda All…ya umurceki ki zauna a cikinsa, kika ki zama a cikinsa. Kuma lallai Amirul muminina ya umurceki ki koma zuwa garinki inda kika fito.

A nan sai ta kara bayyana kiyayyarta ga Amirulmuminina (a), inda ta maiyarwa ibn Abbas Ammsa tna cewa: All..ya jikan Amirulmuminina, shi ne Umar dan Khaddab. Sai ibnu Abbas yace: Haka ne, amma wannan Aliyu dan Abitalib shi ma Amirulmuminina ne.

Sai tace: naki na ki.

Sai  yace: Kinki da hakan, na wani lokaci ne kadan, kamar tatsa da tatsa. Sai ki zama ba zaki iya hallatawa ba, ba zaki haramta ba, ba zaki bada umurnin ba ba zaki hana ba.  

Sai ta karaya da maganarsa, ta zubar da hawayenta sai tace: Haka ne, zan koma, lallai mafi munin gari a waje ne, shi ne garin da kuke zama. Sai ya ce mata: Amma na rantse da All..ba wannan ne ya kamata ya zama sakamakommu daga wajenki ba. Saboda mun sanyaki mahaifiyar muminai…..

Sai ta ce: Kana mani gori da manzon All..(s) ne? sai ya ce: Ee!! muna maki gori da wanda da kina da irinsa da kin mana gori da shi. Sai ya fita ya barta.

Sannan ya koma wajen Amirulmuminina (a) ya fada masa abinda ya faru, da kuma kalaman da suka gudana a tsakaninsu. Har’ila yau da amincewarta da umurninsa na ta koma madina. Sai yace masa ya yi dai dai.

Sannan Imam (a) ya shirya mata Ayari cikakkiya na musamman, a ranar da aka ajiye zata fita sai Imam (a) ya shiga wajenta tare da yayansa Imam Al-Hassan da Al-Hussain (a).

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 127 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 125 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124 August 13, 2025 Iran: Babu Mika Kai Ga Takurawar kasashen Yamma har sai An Kawo Karshen Barazana August 13, 2025 Hukuma Mai Kula Da Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Paris Ya Dakatar Da Wani Ma’aikacinta August 13, 2025 Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy August 13, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi August 13, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
  • Sayyid Huthi Ya Yi gargadi Yiyuwar Tarwatsewar kasashen yankin idan HKI Ta  Tabbaga Shirinta
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126
  • ‘Zan iya shiga mummunan yanayi idan Dangote bai aure ni ba’
  • Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
  • Larijani Ya Ce: ‘Yan Gwagwarmaya Sun San Abubuwan Da Suka Dace
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Ce: ‘Yan Gwagwarmaya Sun San Abubuwan Da Suka Dace
  • Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran