Rootswatch Ta Karrama Builder Muhammad Uba Da Lambar Yabo Ta Kasa
Published: 15th, May 2025 GMT
An karrama Injiniya Dr. Mohammed Uba da lambar yabo ta kasa ta Rootswatch ta shekarar 2025, a matsayin girmamawa bisa gagarumin gudummawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma, aiwatar da muhimman ayyukan raya kasa, da kuma kyakkyawan jagoranci.
An mika wannan lambar yabo ne a yau a Cibiyar Karramawa ta Kasa da Kasa da ke Abuja.
An karrama Dr. Uba tare da wasu shugabannin kananan hukumomi guda uku daga Jihar Jigawa da suka hada da Abdullahi Na Layi, Jarma na Garki, da Malam Madori, saboda hadin gwiwarsu wajen bunkasa ci gaban al’umma tun daga yankunan karkara.
Taron ya jawo hankalin manyan baki daga sassa daban-daban na ƙasar, kuma ya kasance wata hanya ta ƙarfafa gwiwar shugabannin kananan hukumomi wajen ƙara himma a ayyukan da suke yi.
A jawabinsa na godiya, Dr. Uba ya gode wa al’ummar Birnin Kudu bisa goyon bayan da suke ba shi a koda yaushe, tare da alkawarin ci gaba da sadaukarwa wajen hidima ga al’umma.
Ya kuma bayyana godiyarsa ga Gwamna Umar Namadi saboda samar da yanayi mai kyau da ke bai wa kananan hukumomi damar sauya rayuwar al’umma ta hanya mai ma’ana.
Lambar yabon ta sake tabbatar da irin karbuwa da shugabanci nagari ke samu a matakin karkara, tare da haskaka ci gaban da Jihar Jigawa ke samu a ƙarƙashin wannan gwamnati.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Lambar Yabo
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
Gwamnatin Tarayya ta amince a kafa karin sababbin jami’o’i masu zaman kansu guda guda tara a fadin Najeriya.
Ministan Ilimi, Dr Tunji Alausa ne ya sanar da hakan ranar Laraba lokacin da yake jawabi ga ’yan jaridar Fadar Shugaban Kasa jim kadan da kammala taron Majalisar Zartarwa ta Kasa.
Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanciShugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya jagoranci taron wanda aka gudanar a Abuja.
A cewar ministan, sababbin jami’o’in da aka ba lasisin sun hada da Jami’ar Tazkiyah da ke Kaduna, Jami’ar Leadership da ke Abuja, Jami’ar Jimoh Babalola da ke Kwara da Jami’ar Bridget da ke Mbaise a jihar Imo.
Sauran jami’o’in sun hada da jami’ar Greenland da ke Jigawa da jami’ar JEFAP da ke Neja da jami’ar Azione Verde da ke Imo, sai jami’ar karatu daga gida ta Unique da ke jihar Legas da kuma takwararta mai suna American Open University da ke jihar Ogun.
Alausa ya kuma ce Tinubu ya gaji bukatu guda 551 na kafa makarantun gaba da sakandire masu zaman kansu, wadanda ya ce dole sai an cika tsauraran sharuda kafin a ba su lasisin.
Sai dai ya ce rashin cika wadannan sharuda ne ya rage adadin zuwa guda 79 kacal, inda daga ciki aka amince da guda tara a ranar ta Laraba.
Ya ce da yawa daga cikin jami’o’in da aka ba lasisin sun dade suna jira, wasu ma sun shafe sama da shekaru shida suna kan layi.