NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Published: 15th, May 2025 GMT
Ƴan majalisar tarayya guda biyu daga jihar Kano, Kabiru Usman da Abdullahi Sani, sun sanar da barin jam’iyyar NNPP zuwa APC a yayin zaman majalisar ranar Alhamis, suna mai nuni da rikice-rikicen cikin gida na jam’iyyar.
Shugaban majalisar Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙun ficewarsu a zaman majalisar, inda ya bayyana cewa Usman na wakiltar mazabar Rano/Bunkure/Kibiya, yayin da Sani na wakiltar Karaye/Rogo.
Ko da a kwanan baya ma Sanata AbdulRahman Kawu Sumaila da wasu sun fice daga jam’iyyar NNPP, su ma dai sun ce rikicin ne ya fitar da shi.
Shugaban jam’iyyar APC Abdullahi Ganduje da wasu manyan ƙososhin jam’iyyar sun halarci taron sauyin sheƙar a majalisar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Aminu Ɗantata a Kano
An yi wa marigayi Alhaji Aminu Ɗantata jana’izar Salatul ‘Ga’ib’ a garin Kano.
An yi sallar ne a masallacin Umar bn Khattab da ke kan titin Gyadi-Gyadi.
Za a binne Aminu Ɗantata a Madina — Iyalansa Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin ZazzauSheikh Ibrahim Khalil, Shugaban Majalisar Malamai na Jihar Kano, tare da Sheikh Ibrahim Aminu Daurawa, ne suka jagoranci sallar.
Manyan baƙi da dama sun halarci jana’izar, ciki har da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, mambobin majalisar zartarwa na Jihar Kano, manyan ‘yan kasuwa da wasu mutane.
Aminiya ta ruwaito marigayi Alhaji Aminu Dantata, ya rasu a birnin Abu Dhabi, kuma za a birne shi a Madina bayan wasiyyar da ya bari kafin rasuwarsa.
Ga hotunan a ƙasa: