Leadership News Hausa:
2025-08-14@14:58:35 GMT

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

Published: 15th, May 2025 GMT

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

Ƴan majalisar tarayya guda biyu daga jihar Kano, Kabiru Usman da Abdullahi Sani, sun sanar da barin jam’iyyar NNPP zuwa APC a yayin zaman majalisar ranar Alhamis, suna mai nuni da rikice-rikicen cikin gida na jam’iyyar.

Shugaban majalisar Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙun ficewarsu a zaman majalisar, inda ya bayyana cewa Usman na wakiltar mazabar Rano/Bunkure/Kibiya, yayin da Sani na wakiltar Karaye/Rogo.

Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC Gwamna Yusuf Ya Yi Barazanar Ƙwace Lasisin Jerin Gidajen Kwankwasiyya, Amana Da Bandirawo 

Ko da a kwanan baya ma Sanata AbdulRahman Kawu Sumaila da wasu  sun fice daga jam’iyyar NNPP, su ma dai sun ce rikicin ne ya fitar da shi.

Shugaban jam’iyyar APC Abdullahi Ganduje da wasu manyan ƙososhin jam’iyyar sun halarci taron sauyin sheƙar a majalisar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon malami kuma manomi, Andrew Imuekheme, a Jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata a garin Ikabigbo, da ke Masarautar Uzairue, a Ƙaramar Hukumar Etsako ta Yamma.

Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Rahotanni sun ce Malam Andrew na kan hanyarsa daga gona lokacin da maharan suka tare shi, tare da ɗauke shi zuwa daji.

Wata mata da ta tsere daga hannun maharan ta koma cikin gari tare da sanar wa mafarauta, waɗanda suka fara bincike nan take.

Tuni jami’an tsaro suka umarci manoma da ke da gonaki a kusa da yankin da su koma gidajensu saboda tsaro.

Daga baya, ’yan sa-kai sun gano babur da takalman mamacin.

Bayan zurfafa bincike cikin dare suka gano gawarsa.

Sarkin garin, Cif Braimah Alegeh, ya yi Allah-wadai da kisan tare da bayyana mutanensa a matsayin masu zaman lafiya.

Ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.

Wannan shi ne karo na uku da irin wannan kisan ke faruwa a garin.

Shekaru biyu da suka gabata, an kashe wani malamin Katolika da shugaban mafarauta.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce zai fitar da sanarwa daga baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128
  • Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe
  • Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya
  • ‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi
  • Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku
  • Majalisar Kano Ta Karbi Kudirin Karamin Kasafin Kudi Na Shekarar 2025