Iran Ta Nuna Damuwarta Akan Tabarbarewar Harkokin Tsaro A Kasar Libya
Published: 15th, May 2025 GMT
A yau Alhamis ne dai kakakin ma’aikatar harkokin wajen jamhuyriyar musulunci ta Iran Dr. Isma’ila Baka’i, ya bayyana damuwar kasar akan halin da ake ciki a birnin Tripoli na kasar Libya wanda ya yi sanadiyyar kashe mutane masu dama, tare da yin kira da a kawo karshen zubar da jini.
Dr. Baka’i ya yi ishara da nauyin da ya rataya a wuyan dukkanin wadanda suke da hannu a fadace-fadacen da suke faruwa a cikin babban birnin kasar ta Libya, sannan ya bukace su da su taimaka wajen dawo da zaman tsaro a cikin kasar.
Haka nan kuma ya bukace su da su koma kan teburin tattaunawa mai maimakon amfani da karfi, su kuma kaucewa bai wa kasashen waje damar tsoma baki a cikin harkokin cikin gidansu.
Dr. Baka’i, ya kuma mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda rikicin na kasar ta Libya ya rutsa da su, da kuma yin addu’ar samun sauki ga wadanda suka jikkata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
Mai magana da yawun ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ya bayyana a yau Talata 12 ga wata cewa, bisa dokoki ko ka’idojin da suka shafi saka wasu sassa cikin wadanda aka sanyawa takunkumin sayar musu da kayayyaki, ma’aikatar ta fitar da sanarwa mai lamba 21 da ta 22 a ranar 4 da kuma ranar 9 ga watan Afrilun bana, inda ta saka wasu sassa 28 na Amurka cikin wadanda ta sanyawa takunkumin sayar musu da kayayyaki, wato hana sayar musu kayayyakin amfanin jama’a da ake iya amfani da su a bangaren soja. Har wa yau, domin tabbatar da matsayar da aka cimma a wajen shawarwarin manyan jami’an Sin da Amurka a bangaren tattalin arziki da cinikayya, an yanke shawarar cewa, tun daga yau Talata 12 ga watan Agusta, za a ci gaba da dakatar da wannan mataki na tsawon kwanaki 90 ga sassa guda 16 na Amurka da Sin ta sanyawa takunkumin bisa sanarwar ranar 4 ga watan Afrilun bana. Sa’annan ga sassan Amurka 12 da Sin ta sanyawa takunkumin bisa sanarwar ranar 9 ga watan Afrilu, za a daina aiwatar da matakin a kan su.
Jami’in ma’aikatar cinikayya ta Sin ya yi karin haske cewa, idan ’yan kasuwa na bukatar fitar da kayayyaki zuwa ga wadannan sassan Amurka, ya kamata su nemi izini daga ma’aikatar cinikayya ta Sin, wadda za ta binciki batun bisa dokoki da ka’idoji, sannan a ba wadanda suka dace izini. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp