Jami’ar Bayero Zata Horar Da Masu Amfani Da Social Media
Published: 15th, May 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta hada kai da tsangayar sadarwa ta Jami’ar Bayero Kano, domin bayar da takardar shaidar difloma ga masu amfani da shafukan sada zumunta da ke da hannu wajen tallata manufofin Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya bayyana hakan a karshen taron yini biyu da aka gudanar a Kano.
Kwamared Waiya ya ce horon na da nufin inganta yadda mahalarta taron ke amfani da kafafen sada zumunta wajen musayar bayanai da suka shafi ayyukan gwamnati.
“Kwas din diflomasiyyar da aka gabatar zai inganta karfin mahalarta don yin amfani da dandamali na kafofin watsa labarun yadda ya kamata wajen yada bayanai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati,”
Ya bukaci mahalarta taron da su yi aiki da gaskiya tare da bin ka’idojin da’a ta yanar gizo.
“Muna sa ran ku kiyaye martabar gwamnati da kanku, dole ne ku gudanar da ayyukanku cikin girmamawa da da’a, kamar yadda kuke wakiltar wannan gwamnati.” Inji shi.
Waiya ya kuma ƙarfafa su da su yi la’akari da samun kuɗin shiga ta hanyar dandamali na dijital.
“Akwai manyan damar kasuwanci a shafukan sada zumunta. Ina ƙarfafa ku ku yi amfani da su don ƙarfafa kanku da kuma zama masu cin gashin kan ku ta hanyar kuɗi.”
A jawabinsa na rufe taron, Shugaban kungiyar Advocates for Abba Kabir Yusuf Project Promotion na Twitter ya bayyana cewa taron ya kara fadada kwarewarsu tare da zurfafa fahimtar yadda za su bunkasa nasarorin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya samu ta hanyar dabaru.
Taron ya gabatar da zama daga masu jawabai daban-daban. Malam Auwal Sa’id Mu’azu, mai ba da shawara kan harkokin yada labarai da sadarwa, ya gabatar da kasida mai suna “Media Convergence and Artificial Intelligence – A Strength or a Threat to Media Practice.” Aisha Bala Rabi’u ta Kano State Polytechnic tayi magana akan “fahimta da yaki da bata gari, labarai na karya, da dabarun tantance gaskiya,” yayin da Aisar Salihu Fagge ya gabatar da lacca akan “Kirkirar Abun ciki da Tasirin Sakon Social Media.” Umar Sulaiman Usman ya nuna dabarun ƙirƙirar abun ciki.
Ma’aikatar yada labarai da harkokin cikin gida tare da hadin gwiwar Nexa Digital Services ne suka shirya taron.
Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata. Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.
A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.
Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.
A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci